HKI Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Yankin Khan-Yunus
Published: 7th, April 2025 GMT
A rana ta 21 da Isra’ila ta sake komawa yaki da al’ummar Falasdinu a Gaza, jiragen yakinta sun kai hare-hare munanan a yankin Khan-Yunus da ya yi sanadiyyar shahadar mutane da dama, da kuma jikkata wani adadin Falaasidinawa mai yawa.
Jim kadan bayan kai wannan harin ne dai kungiyar ta mayar da martini ta hanyar harba makamai masu linzami akan matsugunin ‘yan share wuri zauna a Asqalan da hakan ya yi sanadiyyar jikkatar ‘yan sahayoniya.
A gafe daya ana gudanar da yajin aiki na gama gari a yankin yammacin kogin Jordan saboda nuna kin amincewa da yadda ‘yan sahayoniya suke yi wa al’ummar Falasdinu kisan kiyashi. Kungiyoyin fararen hula ne su kirayi wannan yajin aikin, wanda ya game yankin na yammacin kogin Jordan.
A wani labarin daga Gaza, ma’aikatar kiwon lafiya ta sanar da cewa da akwai mutanen da sun haura miliyan biyu da suke fama da matsalar rashin abinci mai gina jiki.
Ma’aikatar ta yi wannan sanarwar ne adaidai lokacin da ake raya ranar lafiya ta duniya, tana mai kara da cewa; a kowane lokaci yanayin kiwon lafiya a zirin Gaza yana kara tabarbarewa.” Haka nan kuma ta yi gargadi akan rufe dukkanin hanyoyin shigar da abinci cikin yankin da hakan yake jefa rayuwar yara masu yawan gaske cikin hatsari.
Wani batu da hukumar kiwon lafiya ta yankin na Gaza, ta yi gargadi a kansa, shi ne yadda Isra’ila ta hana a shigar da riga-kafin shan inna cikin yakin, da hakan zai rusa kokarin da aka yin a watanni 7 a baya na fada da wannan cuta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hassan Fadlallah: Amurka ke da alhakin ayyukan wuce gona da iri na Isr’aila a Lebanon
Wani mamba na kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar ta Lebanon ya soki hare-haren da gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila take kai wa a kudancin kasar Lebanon da kuma keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta, yana mai jaddada cewa Amurka ce ke da alhakin kai hare-haren wuce gona da iri na sahyoniyawan.
A cewar Al-Mayadeen, mazauna kudancin kasar Lebanon sun binne gawawwakin shahidan Hizbullah 14 a garin Blida a wani gagarumin biki.
Hassan Fadlallah, wakilin kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar Lebanon ya bayyana a yayin jawabinsa cewa: Gwamnatin Sahayoniya tana cin gajiyar raunin gwamnatin Lebanon ta yi, kuma muna bukatar matsayin da ya kunshi ayyuka na zahiri, hatta a matakin siyasa da diflomasiyya.
Ya kara da cewa: “Muna kira ga gwamnatin Lebanon da kada ta yi watsi da nauyin da ke kanta, kuma idan ta dauki matakin da ya dace, to za mu tsaya tare da ita.” Makiya suna amfani da wasu muryoyi a cikin gida da ke kira ga Isra’ila da su ci gaba da kai hari a cikin Lebanon, Waɗannan ‘yan amshin shata ne kuma za su sha kunya.
Fadlallah ya jaddada cewa: Bai kamata a ci gaba da wannan lamari a kudancin Lebanon ba, kuma Amurka ce ke da alhakin kai hare-haren wuce gona da iri na gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila.
Wannan mamba na kungiyar Hizbullah ya jaddada cewa, babu batun tsro a cikin tafarkin da suke bi, kuma mutanen kudancin Lebanon sun nuna haka a aikace.”