Kasar Sin Ta Nanata Kudurinta Na Ci Gaba Da Bude Kofa Yayin Wani Taro Da Kamfanonin Amurka
Published: 7th, April 2025 GMT
Ya kuma jaddada cewa, manufofin kasar Sin na jan hankalin jari daga waje ba su sauya ba, kuma ba za su sauya ba.
Tattaunawar na zuwa ne yayin da ake tsaka da shiga wani sabon zagayen zullumi dangane da cinikayya a duniya inda a baya-bayan nan Amurka ta kara haraji kan abokan cinikayyarta, ciki har da Sin.
Ling Ji ya soki wannan mataki, yana mai kiransa da wanda ya yi matukar keta ka’idojin tsarin cinikayya tsakanin kasa da kasa, haka kuma ya keta hakkokin sauran kasashe. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Muscat Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Kama Hanyar Zuwa Birnin Domin Ci Gaba Da Tattaunawa Da Amurka
Ministan harkokin wajen Iran ya nufi birnin Muscat na kasar Oman a yau domin gudanar da zaman tattaunawa ba na kai tsaye ba da Amurka
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya sanar da cewa: A yau ne ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya nufi birnin Muscat na kasar Oman a karkashin jagorancin tawagar diflomasiyya da fasaha don shiga zagaye na uku na shawarwarin da ba na kai tsaye ba da Amurka ta hanyar shiga tsakanin mahukuntan Oman.
Baqa’i ya bayyana cewa: Bangarorin biyu sun amince da gudanar da tarukan fasaha tare da halartar manyan jami’an shawarwari, yana mai bayanin cewa “bisa tsarin da Oman ta shirya da kuma hadin gwiwa tsakanin Iran da Amurka, za a gudanar da tarukan fasaha da shawarwari kai tsaye tsakanin ministan harkokin wajen Iran da wakilin shugaban Amurka na musamman a ranar Asabar.”
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Ci gaban da ake samu a shawarwarin yana bukatar daya bangare ya nuna kyakykyawar fahimta, da gaske, da kuma hakikanin gaskiya, yana mai jaddada cewa: Tawagar Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi aiki ne bisa gogewar da ta gabata da kuma dabi’ar daya bangaren, kuma ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen cimma halaltacciyar hakki da muradun al’ummar Iran.