Kungiyar Tsofaffin Ma’aikatan Hukumar Gidan Rediyon Tarayya (FRCN) ta Umarci Mambobinta a Fadin Kasa da Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Kudin Fansa da Aka Yi Alkawari Tsawon Shekaru.

A cikin wata sanarwa, kungiyar ta bayyana cewa zanga-zangar da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba na da nufin jawo hankalin hukumomi masu ruwa da tsaki kan kalubalen da tsofaffin ma’aikata ke fuskanta.

Ana sa ran zanga-zangar za ta fara ne a hedikwatar Gidan Rediyon Najeriya da ke Abuja da misalin karfe goma na safe, sannan ta ci gaba zuwa wasu wurare cikin lumana, yayin da masu shirya zanga-zangar suka bukaci a tabbatar da cikakken daukar rahoton al’amarin daga kafafen yada labarai.

Jagororin zanga-zangar sun nuna rashin jin dadinsu kan zargin gaza biyan kudaden fansa daga Hukumar Tsare-tsaren Biyan Fansho (PTAD), duk da cewa an ce an amince da biliyoyin naira domin biyan su.

Wasu daga cikin tsofaffin ma’aikatan da suka nuna goyon baya ga zanga-zangar sun bayyana mamaki kan irin shiru da kungiyar FRCN na kasa ke yi game da wannan batu mai matukar muhimmanci, wanda bai kamata a ci gaba da dauka da wasa ba, musamman ganin halin kuncin da masu ritaya ke ciki.

Suleiman Kaura

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Samarin Arewa sun yaba wa Sarkin Daura kan bai wa Ja’o’ji muƙami

Gamayyar Ƙungiyoyin Matasan Arewa, sun yaba wa Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruk, bisa bai wa Nasir Bala Ja’o’ji muƙami a Majalisar Zartaswa ta Babbar Kwalejin Ilimi da Fasaha ta Tarayya, Potiskum, da ke Jihar Yobe.

A wata wasiƙar taya murna da shugaban shiyyar ƙungiyar, Makama Dan Kaduna, ya sanya wa hannu bayan wani taro da suka gudanar a Kaduna, sun ce Ja’o’ji mutum ne mai kishin matasa da ƙoƙarin inganta rayuwarsu.

Magidanci ya kashe kansa saboda mutuwar matarsa a Neja An gano tsohuwar da ake nema a cikin maciji

Sun bayyana cewa, “Wannan muƙami da Sarkin Daura zai ba shi, ya ƙara tabbatar da binciken da muka gudanar wanda ya nuna cewa Ja’o’ji yana cikin shugabannin matasa 10 da suka fi fice da kwarjini a jihohin Arewa.”

Ƙungiyar ta kuma jinjina wa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, bisa ƙoƙarinsa wajen inganta rayuwar matasa.

Sun ce, “Nan ba da jimawa ba za mu fitar da sakamakon bincikenmu wanda ya gano 10 ciki har da Nasir Bala Ja’o’ji, da suka yi fice wajen tallafa wa matasa a Arewa. Za mu karrama su ɗaya bayan ɗaya.”

Sun ƙara da cewa, “Samun shugabannin matasa masu jajircewa a wannan yankin babbar albarka ce ga al’ummarmu.

“Hakan na nuna mana cewa akwai kyakkyawar makoma ta ci gaba a Arewa gaba ɗaya.”

Sannan sun bayyana cewa sun aike wa ƙungiyoyinsu a dukkanin jihohi 19 na Arewa goron gayyata domin naɗin sabbin muƙamai a Masarautar Daura.

“Za a gudanar da babban taron karramawa wanda ba a taɓa ganin irinsa ba a nan kusa, domin naɗin sabbin muƙamai da Masarautar Daura za ta yi.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115
  • An kashe sojoji 12 a barikin Nijar
  • Samarin Arewa sun yaba wa Sarkin Daura kan bai wa Ja’o’ji muƙami
  • Yadda Za A Gudanar Da Zaben Sabon Paparoma Da Zai Gaji ‘Pope Francis’
  • Sulhu da ’yan bindigar Katsina: Gaba aka ci ko baya?
  • Sojojin Mamaya Sun Yi Kasan Kiyashi A Zirin Gaza Da Kuma Ci Gaba Da Killace Falasdina  Cikin Masifar Yunwa
  • An Gano Naira Miliyan 27.8 Da Suke Zirarewa A Albashin Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Gano  An Biya Wasu Ma’aikatan Bogi Naira Miliyoyi
  • Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya
  • Zanga-zangar Lumana Wani Bangare Ne Na Mulkin Dimokuradiyya