Aminiya:
2025-04-28@04:09:26 GMT

Saudiyya ta sanya wa masu Umarah wa’adin ficewa daga ƙasar

Published: 8th, April 2025 GMT

Gwamnatin Saudiyya ta ayyana 1 ga watan Dhul Qada, wadda za ta yi daidai da 29 ga watan Afrilu, a matsayin ranar ƙarshe da duk wani baƙo da ke ƙasar da zummar aikin Umarah da ya fice daga ƙasar.

Sanarwar da ma’aikatar aikin Hajji da Umarah ta Saudiyya ta fitar ta ce ta ɗauki matakin ne domin fara gudanar da shirye-shiryen aikin Hajji mai zuwa.

Gobara ta laƙume ƙauyuka a Borno Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 30 a Kongo

Cikin wata sanarwa, ma’aikatar ta ce ranar 15 ga watan Shawwal, da ya yi daidai da 13 ga watan Afrilu, ita ce ranar karshe da masu shiga ƙasar domin aikin Umrah za su daina shiga, sai dai a fita.

Ma’aikatar ta jaddada cewa duk wanda aka samu ya ci gaba da zama a ƙasar har ya wuce lokacin da keɓe, to ko shakka babu ya saɓa ka’ida sannan kuma zai fuskanci hukunci.

Mahukuntan sun buƙaci mutane da ma kamfanonin da ke shirya zuwa aikin Umrah da su kiyaye da waɗannan lokuta da aka ƙayyade.

An kuma yi gargaɗin cewa duk wani jinkiri na barin mutane, ƙasar za a ɗauke shi kamar karya doka.

Ta ce duk kamfanin da aka samu da ƙin bayyana mutanen da suka ƙi koma wa ƙasashensu to za a ci tararsu riyal dubu 100.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Saudiyya Umarah

এছাড়াও পড়ুন:

An sako limamin Katolika da aka sace a Kaduna

An sako limamin cocin Katolika, Rabaran Fada Ibrahim Amos wanda ’yan bindiga suka sace a ranar Alhamis da rana a Kurmin Risga da ke Ƙaramar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna.

Fada Amos, wanda ke aiki a Cocin St. Gerald Ƙuasi Parish ya dawo gida lafiya lau ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 2 na tsakar dare, kwana ɗaya bayan sace shi.

An kama mutum 2 ɗauke da ƙwayar tramadol ta N150m a Kano Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe

Bayani kan sakin nasa na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Shugaban Cocin Diocese na Kafanchan, Rabaran Fada, Dakta Jacob Shanet ya fitar, inda ya gode wa Allah tare da nuna godiya ga al’umma bisa addu’o’i da goyon baya da suka bayar a lokacin da lamarin ya faru.

Fada Shanet ya jinjina wa ƙoƙarin ƙungiyoyin tsaro na gari, ’yan sanda da jami’an DSS da suka ba da gudunmawa a lokacin da aka sace limamin.

Yankin Kudancin Kaduna na daga cikin wuraren da rikice-rikice da garkuwa da mutane suka yawaita.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar ‘Yan Sama Jannati Na Shenzhou 19 Za Su Dawo Doron Kasa A Ranar Talata
  • Falasdinawa 39 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’o’I 24
  • Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’
  • Na shiga fim ne don isar da saƙon Musulunci — Malam Inuwa Ilyasu
  • Gwamnatin Katsina Ta Sauya Masu Yi Wa Alhazai Hidima A Saudiyya
  • Copa Del Rey: Real Madrid Ta Buƙaci A Sauya Alƙalin Wasa A Karawarta Da Barcelona
  • An sako limamin Katolika da aka sace a Kaduna
  • Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya
  • Jigawa Ta Bude Sabon Babi: Maniyyata Za Su San Masaukansu Tun Daga Gida Najeriya
  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)