Hatsarin mota ya kashe mutane 5 a Yobe
Published: 8th, April 2025 GMT
Aƙalla mutane biya ne suka mutu, 19 suka yi munanan raunuka a dalilin hatsarin mota da ya rutsa da su a Kasuwar Damagum da ke kan babbar hanyar Kano-Maidugri a Jihar Yobe.
Lamarin ya auku ne da misalin ƙarfe 1:00 na ranar Lahadi.
Saudiyya ta sanya wa masu Umarah wa’adin ficewa daga ƙasar Gobara ta laƙume ƙauyuka a BornoWani da lamarin ya faru a idonsa, ya shaida wa Aminiya cewa, gudun wuce sa’a da wani direban bas ke yi ne ya janyo hatsarin, inda ya afka wa mutanen da ke tsaye a bakin titi ana tsaka da cin kasuwar.
“Direban ya ɗauko fasinjoji ne zuwa Damaturu, kuma da alamu Potiskum ya nufa,” in ji shi.
Kwamandan hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa reshen Jihar Yobe, CC Livinus Longzen Yilzoom, ya tabbatar da mutuwar mutane biyar, yayin da 19 kuma suka samu raunuka.
Daga nan ne kuma ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, da kuma al’ummar Damagum da Jihar Yobe baki ɗaya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hatsarin mota
এছাড়াও পড়ুন:
Mata Sun Yi Zanga-zanga Kan Yawaitar Satar Mutane A Kogi
Yankin Kogi ta Yamma na fama da matsalar tsaro, inda aka ruwaito wasu mazauna garin Oduape a Ƙaramar Hukumar Kabba Bunu sun gudanar da zanga-zanga a bara domin nuna fargabarsu game da yawaitar sace-sace da kashe-kashe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp