HausaTv:
2025-04-12@22:46:44 GMT

Nijar ta ayyana harshen Hausa a matsayin na kasa

Published: 8th, April 2025 GMT

Jamhuriyar Nijar ta ayyana harshen Hausa a matsayin na kasa, yayin da Faransanci ya zama harshen aiki mai sauki, don haka, Faransanci ba yaren hukuma ne ba.

Matakin dai ya dogara ne da shawarwarin da babban taron kasar ya gabatart a watan Fabrairu, wanda kuma shugaban kasar Janar Abdourahamane Tiani ya amince da shi a ranar 26 ga Maris.

 

A yanzu sabon kundin tsarin mulkin kasar ya jera harsuna goma sha daya da ake magana da su na Nijar, inda ya amince da Hausa a matsayin harshen kasa.  

Harshen Hausa dai shi ne yaren da aka fi amfani da shi a duk fadin Nijar.

A kwanakin baya sabbin hukumomin kasar da ke da suka raba gari da kasar faransa wacce ta yi wa kasar mulkin mallaka, ta fice daga kungiyar bunkasa harshen faransaci ta OIF.

Sannan kuma a baya-bayan nan kasar ta sauya sunayen wasu tituna a birnin Yamai masu dauke da sunayen Faransanci, a wani mataki na kawo karshen duk wata alama ta mulkin mallaka na turawan faransa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Kaddamar Da Bikin Nuna Fina-Finan Sinanci Na CMG Karo Na 5

Yau Alhamis ranar 10 ga wata, an fara “Ranar Sinanci ta MDD” ta shekarar 2025, wato bikin nuna fina-finan Sinanci na babban rukunin gidan rediyo da talabijin na kasar Sin na CMG karo na 5 a hukumance.

 

An kaddamar da bikin bisa hadin gwiwar CMG da kungiyar wakilan kasar Sin na MDD dake birnin Geneva da na sauran kungiyoyin kasa da kasa, da ofishin MDD dake birnin Geneva. Daga cikin shirye-shiryen bikin mai taken “Ziyara A kasar Sin” wato “China Travel” a Turance, an gayyaci jama’ar kasashen duniya da su tsara bidiyo game da ziyararsu a kasar Sin, inda suka nuna kyawawan al’adu da zamantakewar al’umma na kasar Sin, da kuma yanayin bunkasuwar kasa, domin samar wa al’ummomin damar kara fahimtarsu game da kasar Sin. (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Daidaitaccen Tunanin Sin Shi Ne Dabarar Fuskantar Da “Haukar Amurka”
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 17: Tinubu Ya Kare Yadda Gwamnatinsa Ke Tafiyar Da Tsarin Rabon Arzikin Kasa
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  •  Amurka Ta Kai Hare-hare A Yankunan Kasa Yemen
  • Sudan Ta Kai Karar HDL A Gaban Kotun Kasa Da Kasa Ta MDD
  • An Kaddamar Da Bikin Nuna Fina-Finan Sinanci Na CMG Karo Na 5
  • Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa