Saudiyya ta bayar da wa’adin ficewar dukkanin masu aikin Umrah daga kasar
Published: 8th, April 2025 GMT
Gwamnatin Saudiyya ta ayyana 1 ga watan Dhul Qada, wadda za ta yi daidai da 29 ga watan Afrilu, a matsayin ranar karshe da duk wani bako da ke kasar da zummar aikin Umarah da ya fice daga ƙasar.
Sanarwar da ma’aikatar aikin Hajji da Umarah ta Saudiyya ta fitar ta ce ta dauki matakin ne domin fara gudanar da shirye-shiryen aikin Hajji mai zuwa.
Cikin wata sanarwa, ma’aikatar ta ce ranar 15 ga watan Shawwal, da ya yi daidai da 13 ga watan Afrilu, ita ce ranar karshe da masu shiga kasar domin aikin Umrah za su daina shiga, sai dai a fita.
Ma’aikatar ta jaddada cewa duk wanda aka samu ya ci gaba da zama a kasar har ya wuce lokacin da kebe, to ko shakka babu ya saba ka’ida sannan kuma zai fuskanci hukunci.
Mahukuntan sun bukaci mutane da ma kamfanonin da ke shirya zuwa aikin Umrah da su kiyaye da waɗannan lokuta.
An kuma yi gargadin cewa duk wani jinkiri na barin mutane kasar za a dauke shi kamar karya doka.
Ta ce duk kamfanin da aka samu da ƙin bayyana mutanen da suka ki koma wa kasashensu to za a ci tararsu riyal dubu 100.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
-Mun lura da ilimomin harkokin zamaninmu a cikin Alkur’ani
Cikin godiyar Allah, muna mika ziyara ga Shehu Isma’ila Umar Almadda (Mai Diwani) da kuma ban gajiya da gabatar da Tafsirin Alkur’ani mai girma na Azumin Ramadan na bana. Allah ya kai mu na badi albarkar Annabi (SAW) da Shehu (RTA).
Ya Shehi, a Tafsirinka na rana ta bakwai mun ji yadda ka yi bayani na ilimomin kiyaye hadurran hanya da ke kunshe a cikin aya ta 63 ta Suratul Furkan (Sura ta 25), “Wa Ibadur Rahman…”.
Mun kara fahimtar cewa, ayar tana nusarwa a kan tafiya cikin tsari walau sufuri ne na titin mota, ko na jirgin sama ko na ruwa ko jirgin kasa, da dukkan alamomin da ake sakawa na gane hanya da kiyaye aukuwar hadurra na ganganci da sauran ilimomin da suka kunshi dokokin hanya, duka suna nan a karkashin fahimtar ayar. Allah ya saka da alkhairi.
Game da sunan Allah na “Arrahmanu” kuwa, ya kara nuna mana cewa ya kunshi kowane ilimi. Kuma duk masana na sunan na “Arrahmanu” su ne suke zama kwararru na kowane fanni da ke tafiya a kan kasa cikin ilimi da kwarewa. Wallahi, wannan yana nuna mana cewa, mu al’umma musamman ta musulmi mu dage da neman ilimi na kowane fanni saboda inganta rayuwa da aiki da ilimin wajen nuna sanin ya kamata.
Daga misalan da ka kawo na batun hanya, na fahimci cewa, idan alamar hanya ta jar danja ta tsayar da direba shi kuma ya ki tsayawa, ya nuna jahilci ko rashin aiki da ilimin, wanda hakan ne yake sa jami’an da abin ya shafa suke hukunta direbobi masu karya dokokin hanya. Su kuma jami’an, yadda suke fara tambayar mai laifin a game da shin yana da lasisin tuki domin tantance cewa, shi a cikin “Ibadur Rahman” yake ko kuma jahili ne. Idan jahili ne hukuncinsa daban, idan kuma wanda ya san abin ne, watau yana daga cikin “Ibadur Rahman”, har yana da lasisi to hukuncinsa ma yakan fi tsanani, duka ya fahimtar da mu cewa muna da komai a cikin Alkur’ani.
Allah ya saka maka da alheri bisa yadda kuma ka karfafa gwiwar masu mulki har ma da magidanta a kan koyar da duk wadanda suke karkashinsu ilimi, domin tabbas jahilci tamkar mutuwa yake. Idan an ba mutane ilimi shi ne zai zama an raya su, haka nan idan an bar su da jahilci to kuma babu makawa an kashe su.
Muna godiya ya Shehi, Allah ya kara lafiya da nisan kwana.
-Tabbas Ya Kamata Mu Zurfafa Bincikenmu A Cikin Alkur’ani Domin Samun Ci Gaba
Assalamu alaikum. Ya Sayyadi barkanmu da kammala watan Azumin Ramadan, Allah ya amsa ibadunmu ya sa muna cikin ‘yantattun da aka ‘yantar, amin. Hakika bayanin da ka yi a kan yadda ya kamata mu al’ummar musulmi mu kara zurfafa bincike a cikin Alkur’ani domin samar da ci gaban zamani da ake gani a ko ina cikin duniya babban lamari ne mai matukar muhimmanci da ya kamata kasashenmu na musulmi mu mayar da hankali a kai.
Musamman ma, mu kasashen Afirka da muka zama koma baya idan aka kwatanta da sauran yankuna na duniya, ya kamata mu su sake nazarin wayewar zamani da ke kunshe cikin Alkur’ani, wanda hakan zai sanya mu iya yin kafada-da-kafada da manyan kasashen duniya irin su Amurka da China ta fannin ci gaban zamani.
Duk wanda ya san tarihi da kuma ilimi, ya san cewa duk bayanan da wadannan kasashen da suka ci gaba suke takama da su da kundayen da suka mallaka na bayanan ilimi muna nan da su a cikin Alkur’ani, abin da ya kamata a yi shi ne mu fadada bincike na fahimtar zamani a cikin Alkur’ani wanda hakan zai bai wa mu Afirka damar yin kirkire-kirkire da gudanar da sabbin ayyuka na ci gaban zamani.
Yana da kyau yadda muke da yawan mahaddata a Nijeriya, ya zama kasar ta zamo kan gaba wajen zama abar koyi a fannin kawo ci gaban zamani a Afirka da kuma inganta rayuwar ‘yan Afirka. Muna da yakinin cewa, in dai an sa hakan a gaba, tabbas nan da shekaru masu zuwa za mu iya cimma duk burin da muke so mu ga mun cimmawa.
Kuma har ila yau, mun ji dadi a kan kiran da ka yi na a sake nazarin wasu abubuwa na shari’a da ba su da asali a ainihin nassin da Allah ya saukar, domin tabbas abubuwan da Allah ya haramta da hukuncinsa (Muharramatu) kuma ya kulle su da hukunce-hukunce (Muhkamatu) babu wanda ya isa ya kara ko ya rage, kuma Allah bai bar su a dunkule ba, ya yi bayaninsu dalla-dalla.
Yadda aka fara shigo da abubuwa cikin addinin nan tun daga zamanin Sahabbai ya rikita abubuwa da yawa. Wannan ba rashin kunya ba ne ko kadan, muna girmama dukkan Sahabbai wallahi, kuma a cikinsu ne wasu suka tsawatar a kan shigo da abubuwa cikin addinin. Ga misalin Hadisin Ka’abu bin Malik, lokacin da wasu matasa suka ziyarce shi, suka yi masa kirarin girmamawa, suka bukaci ya yi musu hira daga cikin rayuwarsa tare da Annabi (SAW), wanda ya ce, musu “in kun ji na yi shiru ku ma ku yi shiru, yadda kaina ya yi fari (furfura) haka kwakwalwata ta yi, kuma abubuwa ne na yadda muka yi rayuwa da Rasulullahi (SAW). Bari na fada muku duk sai da aka canja su face Sallah (kadai), ita ma ga ta nan kun fara canzawa”. Duk wannan ya nuna cewa, ya kamata mu dawo kan turba ta asali.
Allah ya saka da alkhairi, ya Sayyadi. Wallahi muna godiya sosai, domin mun kuma karu da bayanai a kan abubuwan da Shari’a ke kewayawa a kansu na batun da ya shafi daukar kudi daga nan zuwa nan kamar rabon gado; da tsara Iyali da yadda za a yi aure da rabuwarsa da yadda za a yi tarayya a cikin dangi; da ukuba da hukunci a tsakanin abokan hulda. Haka nan, sauran harkoki irin su kokarin tabbatar da zaman lafiya wanda ya kunshi yadda ake shirya yaki, da sulhu, da zaman lumana; da batun riba da ke bayani a kan tsarin yadda za a gudanar da kasuwanci, sai kuma abubuwan da suka shafi dabi’o’i na ‘yan’adam.
Hakika duk sauran abubuwan da ba wadannan ba, Shari’a ta bar mutane su yi hukunci da abin da ke zamaninsu, na daga kundin tsarin mulki da ake shimfidawa don maslahar al’umma wajen habaka tattalin arziki da raya kasa.
Allah ya kara ilimi da fahimta a cikin wannan addini mai fadi da Manzon Rahama, Annabi (SAW) ya zo mana da shi domin tseratar da al’umma duka sai dai wanda ya ki. Mun gode.
Sako daga Malam Miftahu Adam Zariya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp