Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya ce kasarsa ta yi imani da tattaunawa, amma ba a karkashin wulakanci da kaskanci ba.” Ya jaddada cewa Iran ba ta neman yaki, ko tada zaune tsaye, ko kuma mallakar makamin nukiliya, yana mai kira ga kasashen duniya da su amince da hakan.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne a yammacin Lahadin da ta gabata, yayin wata ganawa da wakilan jam’iyyun siyasa da manyan kungiyoyi a kasar, inda ya tattauna batutuwan da suka shafi sauye-sauyen harkokin mulki, da manufofin harkokin waje, da kalubalen tattalin arziki da zamantakewar kasar.

Da yake magana game da kalubalen gudanar da harkokin mulki, shugaban na Iran ya bayyana cewa, ba za a iya cimma gyara halayen kungiyoyi da bangarorin gwamnati ta hanyar canza daidaikun mutane ba, sai dai hakan yana bukatar “sauyi na dabi’un hukumomi na dogon lokaci,” yana mai jaddada cewa, “sauyi na hakika yana daukar shekaru goma.

Dangane da batutuwan da suka shafi zamantakewa, Pezeshkian ya jaddada cewa ba za a iya magance rikice-rikice ta hanyar ba da umarni kadai ba, yana mai bayanin cewa gwamnati na da shirye-shirye don magance matsalolin da suka hada da karancin makarantu, tsadar rayuwa, rashin aikin yi, da rashin daidaiton tattalin arziki, amma “bai takaitu ga samar da shirye-shirye kawai ba.

Dangane da manufofin ketare kuwa, ya yi nuni da cewa, Iran ta tattauna da dukkan shugabannin kasashen yankin a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan Sallah, inda ya jaddada cewa, dangantakar da ke tsakaninta da kasashen da ke makwabtaka da ita ta inganta idan aka kwatanta da baya.

Amma ya kara da cewa, “Tattaunawa da Amurka wani lamari ne na daban,” yana mai bayanin cewa, “Lokacin da Washington ta matsa mana lamba kuma ta ci gaba da barazanarta, ta yaya za mu yi shawarwari da ita?”

Shugaban na Iran ya yi nuni da cewa, matsayin kasarsa na lumana kan amfani da makamashin nukiliya, ba wai kawai maganganun siyasa ba ne, a’a, a maimakon haka a kan wata fatawa ta addini da Jagoran juyin juya halin Musulunci ya fitar ne, wadda ta haramta amfani da makamashin nukiliya ta hanyoyi da ba na ayyukan farar hula ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jaddada cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Amurka Yace Yana Kokarin cimma yarjeniya da kasar China Dangane da Tiktok

Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bada sanarwan cewa yana kokarin cimma matsaya da kasar Chaina dangane da kamfanin sadarwa da kuma yanar gizo na TIK Tok.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shugaban yana fadar haka a shafinsa na ‘Trump Social,

Labarin ya kara da cewa shugaban yana fadar haka a dai dai lokacinda gwamnatin Amurka ta dorawa kayakin kasar China masu shigowa Amurka kudin fito na kasha 125%.

Tun zagaye na farko na shugabancinsa ne shugaban ya fara rigima da kamfanin Tiktok na kasar China wanda ya sami karbuwa a cikin Amurka da kuma kasashen duniya da dama. Amurka tana ganin shafin yanar gizo na tiktok barzane ce ga tsaron kasar Amurka. Kuma har ta bukaci kasashe kawayenta a duniya su daina mafani da Tiktok.

A zangon shugabancinsa na farko dai shugaban ya haramta wayar tafi da gidanka mafi girma a kasar Chaina wato hawawi da kuma kamfanin internet na G%. wadanda yake ganin barazana ne da tsaro da kuma bangaren tattalin arziki ga kasar ta Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  •  Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa
  • Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron   Kan Iyakar Kasashen Biyu
  • Shugaban Kasar Amurka Yace Yana Kokarin cimma yarjeniya da kasar China Dangane da Tiktok
  • Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
  • Jami’an Amurka da na Saudiyya sun tattauna batutuwan da suka shafi Gaza da yankin
  • Pezeshkian : Jagora bai shi da adawa da Amurkawa masu zuba jari a Iran