Aminiya:
2025-04-12@21:09:12 GMT

Arsenal ta gasa wa Madrid aya a hannu

Published: 9th, April 2025 GMT

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal ta lallasa Real Madrid a daren nan a karawar da suka yi ta kwata-fainal a Gasar Zakarun Turai.

Arsenal dai ta doke Real Madrid da ci 3-0 a fafatawar da suka yi a filin wasa na Emirates da ke Landan.

Boko Haram na sake ƙwace ikon wasu yankuna a Borno — Zulum Kisan Isuhu Yellow: ’Yan bindiga sun kai harin ɗaukar fansa

An kammala minti 45 na karawar babu ci, sai dai alƙaluma sun nuna Arsenal ta kai farmaki sau huɗu yayin da Real ta kai hari sau biyar.

Duk da cewa babu ɓangaren da ya samu nasarar zura ƙwallo amma wasan wanda Irfan Peljto na ƙasar Bosnia Herzegovina ya yi alƙalanci ya yi matuƙar zafi tsakanin ɓangarorin biyu.

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne ɗan wasan tsakiya na Arsenal, Declan Rice ne ya zura ƙwallon farko a minti na 58 ta hanyar bugun tazara bayan da ’yan wasan Madrid suka yi wa Bukayo Saka ƙeta.

A minti na 70 ne Declan Rice ya ƙara zura ƙwallo ta biyu a ragar Real Madrid ta hanyar bugun tazara kamar yadda ya yi a karon farko.

A yayin da aka ci gaba da ɗauki ba daɗi ne Mikel Merino ya zura ƙwallo ta uku a minti na 75 da take wasa, bayan ɗan wasa Lewis Skelly ya zuro masa ƙwallon daga gefe.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arsenal

এছাড়াও পড়ুন:

Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa

Shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, ya ce kasarsa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa nan da watanni masu zuwa.

Ya ce hakan na iya faruwa a farkon watan Yuni nan wannan shekarar a taron Majalisar Dinkin Duniya da za a gudanar a New York.

kawo yanzu, Kasashe 147 ne suka amince da yankin na Falasdinawa a matsayin kasa mai yanci.

Kasashen Sifaniya da Ireland da Norway su ne na baya-bayan nan da suka nuna amincewarsu a watan Mayun bara da yankin na Falasdinawa a matsayin kasa mai yanci, matakin da ya fusata Isra’ila.

Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa da dama dai na ganin samar da kasashe guda biyu Falasdinu da Isra’ila shi ne gimshikin samar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 108
  • Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto
  • Darasi daga rayuwar Dakta Idris AbdulAzeez Dutsen Tanshi
  • An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe
  • Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa