HausaTv:
2025-04-12@21:16:14 GMT

An kori jakadan Isra’ila a Habasha daga taron Tarayyar Afirka

Published: 9th, April 2025 GMT

An kori jakadan Isra’ila a Habasha Avraham Neguise daga taron kungiyar Tarayyar Afirka da aka gudanar a wannan Talata a Addis Ababa domin tunawa da kisan kiyashin da aka yi a Rwanda.

An fitar da Neguise daga dakin taro na Mandela da ke hedikwatar Tarayyar Afirka bayan da kasashe da dama suka nuna rashin amincewarsu da halartarsa a taron shekara-shekara kan kisan kiyashin da aka yi a kasar Rwanda.

Jakadan na Isra’ila ya shiga wurin taron ne ba zato ba tsammani, ba tare da an gayyace shi ba, a cewar majiyoyin diflomasiyyar da suka halarci taron.

Majiyar ta kara da cewa tawagogin kasashen Afirka da dama sun nuna rashin amincewa da zuwansa, lamarin da ya sa aka dakatar da taron har sai da ya fita.

Rahotanni sun ce kungiyar Tarayyar Afirka na gudanar da bincike domin gano wanda ya gayyace shi.

Kungiyar fafutukar neman ‘Yancin Falasdinu (PLO) ita ce kungiya ta farko da aka baiwa matsayin mamba mai sa ido a cikin  Tarayyar Afirka a shekarar 1973, kuma tana ci gaba da samun goyon baya mai karfi daga yawancin kasashen Afirka.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Tarayyar Afirka

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron   Kan Iyakar Kasashen Biyu

Sojojin kasa na kasashen Iran ta Armenia sun fara atisayen soje na hadin guiwa a tsakaninsu, don kyautata tsaro na kan iyakar kasashen biyu na kuma tsawon kwanaki biyu.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ne suke jagorantar wannan atisayen. Da nufin hana fasa korin muggan kwayoyi da kuma sulalewar yan ta’adda suka kan iyakokin kasashen biyu.

Burgediya Janar Sayyid Mortaza Mira’in babban hafsan  sojojin kasa na IRGC ya bayyana cewa, wannan atisayennn   yana nuna irin yadda sojojin IRGC suke da shirin kare kasar daggga duk wata barazana. Da kuma abota da kyautata makobtaka da kasashe mmmakobta.

Labarin ya kara da cewa ana gudanar da rawan dajin ne a kan kan iyakar kasashen biyu na nordooz.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
  • Hizbullah ta kirayi gwamnatin Lebanon da ta dauki mataki kan hare-haren Isra’ila
  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 17: Tinubu Ya Kare Yadda Gwamnatinsa Ke Tafiyar Da Tsarin Rabon Arzikin Kasa
  • Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron   Kan Iyakar Kasashen Biyu
  • Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
  • E.U.  ta dauki wasu sabbin matakan kalubalantar harajin fito na Amurka
  • Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa
  • Malaman Makarantun Firamare 1,800 Sun Samu Horo Aka A Kwara