Likitocin Nijeriya dubu 16 sun yi ƙaura zuwa ƙetare — Ministan Lafiya
Published: 9th, April 2025 GMT
Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Pate ya bayyana cewa, sama da likitoci dubu 16 sun fice daga Nijeriya a cikin shekaru biyar zuwa bakwai da suka gabata zuwa wasu ƙasashen duniya don ci gaba da aiki cikin ingantaccen yanayi.
Farfesa Pate ya bayyana haka ne a wurin taron horas da Ƙungiyar Likitocin Afrika da ya gudana a birnin Abuja a ranar Talata.
Ministan ya bayyana cewa, ana ci gaba da samun wani adadi mai yawa na ƙwararrun likitocin da ke da burin fita zuwa wasu ƙasashen duniya aiki, suna fakewa da matsalolin tattalin arziƙi da rashin kyawun yanayin aiki da kuma samun cikakken horo, baya ga zurfafa gudanar da bincike a ƙasashen na ƙetare.
Kodayake ya ce, ficewar ƙwararrun likitoci daga ƙananan ƙasashe zuwa ƙasashen da suka ci gaba, ba sabon labari ba ne, amma sai dai adadinsu na ƙara yawaita a shekarun baya-baya nan a cewarsa.
Pate ya kuma bayyana takaicinsa kan yadda su ma nas-nas da unguwarzoma suka fice daga ƙasar, lamarin da ya ƙara zabtare adadin ma’aikatan lafiyar da ake da su a Najeriya.
A cewar Ministan Lafiyar, kididdiga ta nuna kusan likitoci huɗu ne ke duba mutum dubu 10 a ƙasar, yana mai ƙiyasta sama da Dala dubu 21 a matsayin kuɗin da ake kashe wa kowanne likita guda wajen horas da shi.
“A Najeriya kaɗai, sama da likitoci dubu 16 aka ƙiyasta sun fice daga ƙasar a cikin shekaru biyar zuwa bakwai. Nas-nas da unguwarzoma su ma sun yi ƙaranci.
“Yanzu likita kusan huɗu ne ke duba mutum dubu 10, adadin da ya yi ƙasa sosai idan aka kwatanta da alkaluman da aka amince da su a matakin duniya.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Sakkwato na biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 – NLC
Ƙungiyar Ƙwadago a Jihar Sakkwato (NLC), ta musanta iƙirarin da shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta ƙasa (NULGE), Ali Kankara, ya yi cewa gwamnatin jihar ba ta fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000 ba.
Shugaban NLC na jihar, Kwamared Aliyu Abdullahi, ya bayyana wa manema labarai a ranar Laraba cewa Gwamnatin Sakkwato ta fara biyan sabon albashin tun a watan Janairu ga dukkanin ma’aikatan jihar, ciki har da na ƙananan hukumomi.
Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a KebbiYa ce: “Sakkwato ce jiha ta farko da ta fara biyan sabon albashi na dubu 70, kuma ma’aikatan gwamnati da na ƙananan hukumomi na amfana da shi.
“Maganar shugaban NULGE na ƙasa ba gaskiya ba ce.”
Ya ƙara da cewa bai kamata shugaban NULGE ya faɗi irin wannan magana ba tare da ya bincika gaskiyar al’amari ba.
Kwamared Aliyu, ya yaba wa Gwamna Ahmad Aliyu bisa ƙoƙarinsa na biyan ma’aikata haƙƙoƙinsu da kuma dawo da kuɗin tafiyar da ofisoshi, biyan bashin fansho da sauran haƙƙoƙin ma’aikata.
Sai dai wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa ba dukkanin ma’aikatan ƙananan hukumomin jihar ne ke karɓar albashin dubu 70 ba.
Wani ma’aikaci ya ce: “Wasu daga cikinmu da muke karɓar dubu 18 a da, yanzu muna karɓar dubu 30, yayin da waɗanda ke karbar dubu takwas a baya, yanzu gwamnati na biyansu dubu 20.”
Wannan ya nuna cewa duk da gwamnati na ƙoƙarin biyan sabon albashi, har yanzu ba a kai ga kowa ya samu dubu 70 ba a matakin ƙananan hukumomi.