Iran ba ta amince da Amurka ba, amma za ta gwada su (Araghchi)
Published: 9th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya ce Amurka na da masaniya kan irin karfin kare kai da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ke da shi, yayin da ya ce kasar ta shirya tsaf domin kare kanta.
Ya kuma jaddada cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta yarda da Washington ba, amma duk da haka za ta gwada ta yayin tattaunawar da za a yi nan gaba a ranar Asabar mai zuwa,” in ji Abbas Araghchi yayin wani taron manema labara a Aljeriya.
Babban jami’in diflomasiyyar ya bayyana cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta neman yaki, amma idan ya zama dole ta san yadda za ta kare kanta. »
“Muna shakkar aniyar Amurka kuma ba mu da tabbacin cewa suna da niyyar gudanar da tattaunawa ta gaske, amma za mu gwada su.”
Kalaman na baya-bayan nan sun shafi tattaunawar da ake sa ran za a fara tsakanin Araghchi da manzon Amurka na yankin Steve Witkoff a Muscat babban birnin kasar Omani ranar Asabar tare da ministan harkokin wajen Omani Badr bin Hamad Al Busaidi a matsayin mai shiga tsakani.
Haka nan kuma jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi watsi da zargin kasashen yamma – karkashin jagorancin Washington – cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran na neman mallakar makamin nukiliya.
Ya ce zargin da ake yi wa Iran na neman mallakar makamin nukiliya, zargi ne mara tushe.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Jamhuriyar Musulunci ta Iran
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron Kan Iyakar Kasashen Biyu
Sojojin kasa na kasashen Iran ta Armenia sun fara atisayen soje na hadin guiwa a tsakaninsu, don kyautata tsaro na kan iyakar kasashen biyu na kuma tsawon kwanaki biyu.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ne suke jagorantar wannan atisayen. Da nufin hana fasa korin muggan kwayoyi da kuma sulalewar yan ta’adda suka kan iyakokin kasashen biyu.
Burgediya Janar Sayyid Mortaza Mira’in babban hafsan sojojin kasa na IRGC ya bayyana cewa, wannan atisayennn yana nuna irin yadda sojojin IRGC suke da shirin kare kasar daggga duk wata barazana. Da kuma abota da kyautata makobtaka da kasashe mmmakobta.
Labarin ya kara da cewa ana gudanar da rawan dajin ne a kan kan iyakar kasashen biyu na nordooz.