Leadership News Hausa:
2025-04-12@21:20:55 GMT

Babu Kuɗin Fansar Da Aka Biya Wajen Ceto Janar Tsiga – DHQ

Published: 9th, April 2025 GMT

Babu Kuɗin Fansar Da Aka Biya Wajen Ceto Janar Tsiga – DHQ

Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ba a biya kuɗin fansa ba kafin a ceto tsohon shugaban NYSC, Janar Mahrazu Tsiga (mai ritaya), daga hannun ‘yan bindiga.

A wata sanarwa da Birgediya Janar Tukur Gusau ya fitar, ya bayyana cewa an yi amfani da bayanan sirri da kuma dabarun soji wajen ceto Janar Tsiga.

Dole Dukkanin Masu Umrah Su Fice Daga Saudiyya Kafin 29 Ga Afrilu – Hukumomi An Buɗe Sabbin Cibiyoyin Kula Da Masu Cutar Sankarau A Jihohi 6

An yi garkuwa da shi ne a mahaifarsa Tsiga da ke ƙaramar hukumar Bakori a Jihar Katsina, ranar 5 ga watan Fabrairu, tare da wasu mutane 13.

Sojoji sun gudanar da samame a yankunan Ɗanmusa, Faskari da Kankara, inda ake tunanin ‘yan bindigar ke ɓuya, har suka samu nasarar ceto shi ba tare da biyan fansa ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Janar Tsiya

এছাড়াও পড়ুন:

UBEC Ta Bayyana Jihar Jigawa A Matsayin Abin Kuyi A Fannin Ilimi

Hukumar ilimin bai daya ta kasa wato UBEC ta yabawa Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa bisa jajircewar sa wajen inganta ilimi a matakin farko a Jihar.

Shugabar Hukumar, Hajiya Aisha Garba, ta bayyana hakan a yayin ziyarar gwamnan zuwa hedikwatar UBEC a Abuja.

Hajiya Aisha Garba ta bayyana jihar Jigawa a matsayin abin koyi ga sauran jihohin kasar nan.

Kazalika, ta jaddada irin yadda gwamnati ta zage damtse wajen zuba jari a harkar ilmi, tana mai cewa Jihar ta karɓi fiye da Naira biliyan 21 daga tallafin UBEC tun daga shekarar 2004, wanda ya sanya ta cikin jihohin da suka fi cika sharudan samun tallafin UBEC.

Ta kuma lissafa wasu daga cikin nasarorin da aka cimma a ƙarƙashin Gwamna Namadi wadanda suka hada da gina fiye da ajujuwa 3,000 da rijiyoyi 500 da daukar malaman makaranta fiye da 7,000.

Tace Gwamnatin ta kuma horas da malamai sama da 17,000 da kaddamar da Kungiyoyin Iyaye Mata da Ƙarfafa Kwamitocin Gudanarwar Makarantu wato SBMC da kuma kulla haɗin gwiwa da wani kamfani a shirin Jigawa UNITES.

A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya jaddada cewar, gwamnatin sa ta himmatu wajen sauya tsarin karatu da inganta sakamako ta hanyar amfani da bayanai da kuma haɗa kai da al’umma.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13
  • An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa
  • 2027: Masu Shirin Yin Kawance Na Duba Yiwuwar Zakulo Dan Takarar Da Zai Yi Wa’adi Daya
  • UBEC Ta Bayyana Jihar Jigawa A Matsayin Abin Kuyi A Fannin Ilimi
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  • Babu Wani Saɓani Tsakanin Tinubu Da Shettima — Jigon APC
  • Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet
  • Rundunar Sojan Nijeriya Ta Fara Gasar Wasanni A Sakkwato
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 10, Sun Kashe Ɗan Bindiga 1 A Katsina
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Kashe Ɗan Bindiga A Katsina