A ci gaba da kokarinsa na kawo sabon tsari domin inganta harkokin noma a jihar Jigawa, Gwamna Malam Umar Namadi ya jagoranci tawagar gwamnatin jihar zuwa wani babban taro da manyan masu zuba jari na duniya da masu ruwa da tsaki a harkar noma. Taron wanda ya gudana jiya Talata a otal din Hilton da ke Abuja, ya kunshi wakilai daga kamfanonin SINOMACH, China CAMC Engineering Company Ltd, YTO Group Corporation, da Agra Consortium Ltd, da kuma asusun bunkasa noma na gwamnatin tarayya (NADFUND).

Kyautar LEADERSHIP Ta Kara Zaburar Da Mu Kan Sauke Nauyin Al’ummar Jigawa Akanmu – Gwamna Namadi Kasar Sin Na Yaki Da Cin Zalin Da Amurka Ke Yi Ta Hanyar Dora Haraji Ne Bisa Sanin Ya Kamata Taron ya samar wa Gwamnatin Jihar Jigawa wani dandali na baje kolin kayayyakin gona da jihar ta yi fice akansu ga masu saka hannun jari, wanda ya bayyana tsare-tsaren kawo sauyi da nufin mayar da Jihar Jigawa a matsayin babbar cibiyar kasuwancin kayayyakin gona da bunkasa masana’antu a Nijeriya. Jihar na fatan samun hannun jari a bangaren Kamfanin hada takin zamani domin inganta harkar noma, kamfanin harhada Motocin noma na YTO, aiwatar da aikin noman rani a fadin hekta 600 da ke Hadejia, kamfanin Integrated Halal Products Hub, Mayankar dabbobi ta zamani mai karfin yanka dabbobi 2,500 a kullum da dai sauransu. Tunda farko, a nasa jawabin, Gwamna Namadi ya yi maraba da tawagogin manyan kamfanoni da suka zo don halartar taron baje kolin kayan gona na jihar Jigawa a babban birnin tarayya Abuja. Gwamna Namadi ya jaddada amfanin noma na Jigawa, inda ya ce kashi 80 cikin 100 na kadada miliyan 2.47 na jihar gonaki ne na noma, wanda ya hada da ruwa 242 da kuma Kasuwar Dabbobi ta Maigatari, wacce babu sama da ita a Afirka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

UBEC Ta Yaba Wa Jigawa Kan Inganta Harkar Ilimi A Jihar

Wadannan ayyuka domin inganta harkar ilimi da kuma nuna gaskiya, sun sa Jigawa ta zama abin koyi ga sauran jihohi.

 

Tunda farko, Gwamna Malam Umar Namadi, a nasa jawabin, ya ce gwamnati ta dauki kwakkwaran matakai na magance matsalar rashin ilimi bayan wani bincike da wani masani mai zaman kansa ya fitar cewa, yawancin daliban firamare ba su iya karatu ko rubutu yadda ya kamata.

 

Ya bayyana cewa, an dauki malamai sama da 7,000 a karkashin gwamnatinsa domin karfafa ilimin boko, ya kuma ce jihar ta bullo da sabbin dabaru da suka shafi al’umma, kamar taron iyaye mata da kuma farfado da kwamitocin gudanarwa na makarantu (SBMC), domin inganta zuwan yara makarantu da kuma lura da yadda malamai suke aiki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
  • Gwamna Namadi Na Jihar Jigawa Ya Cancanci Karramawar LEADERSHIP – Hamisu Gumel
  • UBEC Ta Bayyana Jihar Jigawa A Matsayin Abin Kuyi A Fannin Ilimi
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya
  • UBEC Ta Yaba Wa Jigawa Kan Inganta Harkar Ilimi A Jihar
  • Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet
  • Pezeshkian : Jagora bai shi da adawa da Amurkawa masu zuba jari a Iran
  • Malaman Makarantun Firamare 1,800 Sun Samu Horo Aka A Kwara