Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya bayyana cewa JMI ba zata taba jada baya a kan shirinta na makamashin Nukliya ba, kuma yayi allawadai da duka wani shiri na kaiwa cibiyoyin nukliyar kasar Hare-hare.

Tashar talabijin ta Presstv ta nakalto shugaban yana fadar haka a taron raya ranar Nukliya ta karo karo na 19 a wanda aka gudanar a nan Tehran.

Shugaban ya kara da cewa, Iran bata neman yaki da kowa, amma zata maida martani kan duk wata takala daga HKI ko Amurka. Ya ce Iran ba zata amince wani ya hana mutanen kasar amfani da fasahar da All..ya hore masu ba. Ya kuma kara jaddada cewa JMI bata neman mallakar makaman Nukliya.

A rana irin ta yau ce wato 9 ga watan Afrilun shekara ta 2006, masana fasahar nukliya na JMI suka sami nasara a karon farko suka samar da makamashi daga fasahar nukliya tare da amfani da sinadarin Uranium.

A yau shekaru 19 kenan tun lokacin kasar take samun ci gaba a fasahar Nukliya da kuma amfaninsa. Inda ya ma kasar ta kaddamarda sabbin ci gaban da ta samu tare da amfani da makamacin Nukliya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan

Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadaccen Abinci, Sanata Abubakar Kayri ne ya bayyana a haka, a cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar.

“Mun samar da tsarin samar da wadataccen abinci a kasar nan, wanda kowanne dan kasar zai amfana da shi”, in ji Kyari.

Daga cikin manyan abubuwan da suka hada da bashin sun hada da; samar da ingantaccen Irin Shinkafa da kuma habaka yadda ake samar da Irin na Shinkafar.

Sauran sun hada da mayar da hankali wajen yin girbin mai kyau, samar da nau’ikan Shinkafar da ke jurewa kowacce irin cutar da ke lalata Irin Shinkafar da aka shuka, aka ajiye a cibiyar gudanar da bincike kan amfanin gona (NCRI) da ke yankin Badeggi a Jihar Neja.

Kazalika, akwai kuma bukatar kara bunkasa kayan aikin gona, inganata aikin malaman gona, amfani da kayan aikin gona na kimiyya domin rika samar da bayanai a kan lokaci, musamman wanda ya shafi sauyin yanayi, samar da farashin kayan amfanin gona a kasuwa, dakile barkewar kwarin da ke lalata amfanin gona da sauransu.

A nasa jawabin, Karamin Minista a Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Dakta Abdullahi Sabi Abdullahi, ya bayyana gamsuwar da cewa, shuka ingantaccen Irin noma zai taimaka wajen ciyar da daukacin ‘yan Nijeriya gaba.

Dakta Abudullahi ya kara da cewa, ingantancen Iri shi ne, kashin bayan da zai kawo karshen kalubalen da bangeren samar da wadataccen abinci a kasar.

“Wannan hadaka za ta kara karfafawa, musamman kananan manoma na kasar nan guiwa, ta hanyar yin amfani da aikin karfafa wa kanannan manoma gwiwa, wato SHEP, wanda a yanzu aikin ya karade jihohi 14 na kasar nan”, a cewar Abdullahi.

Kazalika, wannan hadakar ta kasance tamkar cike wani gibi ne a tsakanin gudanar da bincike, yin aiki a aikace tare kuma da samar wa manoman kasar nan kayan aikin gona na zamani da kuma samar musu da ilimin kwarewar da ya kamata a fannin na aikin noma.

Shi kuwa, Darakta Janar na Hukumar, wanda kuma shi ne har ila yau, ya jagoranci tawagar kasar ta Japan, Takao Shimokawa ya bayyana cewa, Hukumar ta JICA da kuma Kasar Japan, sun mayar da hankali wajen ganin an bunkasa bangaren noman Shinkafa a Afirka, musamman ma a Nijeriya, duba da cewa, kasar ta kasance kan gaba wajen noman Shinkafa.

Wannan shirin ya nuna a zahiri irin mayar da hankalin da gwamnatin tarayya da Hukumar JICA suka yi, don kara habaka bangaren samar da wadataccen abinci a kasar nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Vietnam Da Malaysia Da Cambodia
  • Iran: Akwai damammaki na diflomasiyya da za mu jarraba aniyar Amurka a kansu
  • Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron   Kan Iyakar Kasashen Biyu
  • Shugaban Kasar Amurka Yace Yana Kokarin cimma yarjeniya da kasar China Dangane da Tiktok
  • Ministan harkokin wajen Iran ya tattauna da takwaransa na Masar kan halin da ake ciki a yankin
  • Pezeshkian : Jagora bai shi da adawa da Amurkawa masu zuba jari a Iran