Rundunar ‘yan sandan Jihar Zamfara ta tabbatar da wani mummunan hari da ‘yan bindiga suka kai a garin Banga, da ke cikin karamar hukumar Kauran Namoda, inda aka kashe mutane biyu tare da sace wasu da dama.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda ta jihar, DSP Yazid Abubakar, ne ya bayyana hakan cikin wata tattaunawa ta wayar tarho da wakilinmu da ke Gusau, babban birnin jihar.

DSP Abubakar ya ce bincike na ci gaba da gudana domin gano adadin mutanen da aka sace a harin.

Ya tabbatar da cewa ana kokari don ganin an ceto mutanen da aka sace cikin koshin lafiya.

Yazid ya kara da cewa an kara kaimi wajen daukar matakan tsaro domin hana faruwar irin wannan lamari a nan gaba.

Shaidu sun shaida wa Rediyon Najeriya cewa maharan sun farmaki garin ne da misalin tsakar dare a ranar Laraba, inda suka buda wuta daga wurare da dama, lamarin da ya haifar da firgici ga mazauna garin.

Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi ta barna na tsawon sa’o’i, inda suka kashe wani dattijo da wata yarinya ‘yar shekara 18 mai suna Amina.

Ya ce da farko maharan sun sace kimanin mutane 26, amma ba su samu nasarar guduwa da su baki daya ba, sakamakon hanzarin da jami’an tsaro da ‘yan sa-kai suka yi.

Wakilinmu ya samu rahoton cewa hadin gwiwar jami’an tsaro da ‘yan sa-kai ya kai ga kashe wasu daga cikin ‘yan bindigar, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga. An kuma tabbatar da cewa maharan sun kasa guduwa da shanun da suka sace.

A cewar shaidu, jami’an tsaro da taimakon jiragen saman rundunar sojin saman Najeriya sun toshe hanyar da maharan ke kokarin tserewa ta kusa da kauyen Yamutsawa.

 

Daga Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hari Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe

Rundunar ’yan sandan Jihar Yobe ta samu gagarumar nasara a ƙoƙarinta na yaƙi da miyagun laifuka, inda ta cafke wasu fitattun mutane biyu da ake zargi da garkuwa da mutane.

Waɗanda aka kama sun haɗa da: Babaro Baushe mai kimanin shekara 40 da Umaru Dau’a, mai kimanin shekara 25 da suka fito daga ƙauyen Askuwari a ƙaramar hukumar Tarmuwa a ranar 9 ga Afrilu, 2025.

Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi

A takardar sanarwar da kakakin rundunar ‘Yan sandan Yobe, SP Dungus Abdulkareem ya fitar ya ce, hedikwatar ’yan sanda reshen Dapchi da misalin ƙarfe 0500hrs, 9 ga Afrilu, 2025, ta cafke waɗanda ake zargin, ’yan ƙungiyar da suka ƙware wajen yin garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa da kuma neman barace-barace, suna gudanar da ayyukansu a ƙananan hukumomin Dapchi da Tarmuwa.

An dai alaƙanta waɗanda ake zargin da laifuka da dama da suka haɗa da: A ranar 21 ga Nuwamba, 2024, masu garkuwar sun kai hari ƙauyen Badegana da kuma kai hari gidan wani da aka kashe, wanda ya yi sanadin rasa rai.

A ranar 10 ga Maris, 2025, waɗanda ake zargin sun karɓe N250,000 da ƙarfi daga Mudi Ibrahim na ƙauyen Askuwari, ƙaramar hukumar Tarmuwa, bayan sun yi barazanar sace shi ko kuma su kashe shi.

Waɗannan mutane sun amsa laifukan da suka aikata, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike a sashin bincike na jihar (SID).

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado  ya ba da umarnin ci gaba da ƙoƙarin kama wasu ’yan ƙungiyar kuma ya buƙaci al’umma da su bayar da sahihan bayanai don taimakawa wajen gudanar da bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno
  • ‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Mamaye Sassan Jihar Borno -Zulum
  • Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto
  • ’Yan bindiga sun harbi alkali da ɗansa, sun sace mutane 13 a Katsina
  • Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar
  • Sabon Kwamishinan Na Kwara Ya Sha Alwashin Dakile Laifuka
  • An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe
  • An Sace Dalibin Jami’ar Tarayya Birnin Kebbi
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Kashe Ɗan Bindiga A Katsina