HausaTv:
2025-04-12@21:31:55 GMT

Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa

Published: 10th, April 2025 GMT

Shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, ya ce kasarsa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa nan da watanni masu zuwa.

Ya ce hakan na iya faruwa a farkon watan Yuni nan wannan shekarar a taron Majalisar Dinkin Duniya da za a gudanar a New York.

kawo yanzu, Kasashe 147 ne suka amince da yankin na Falasdinawa a matsayin kasa mai yanci.

Kasashen Sifaniya da Ireland da Norway su ne na baya-bayan nan da suka nuna amincewarsu a watan Mayun bara da yankin na Falasdinawa a matsayin kasa mai yanci, matakin da ya fusata Isra’ila.

Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa da dama dai na ganin samar da kasashe guda biyu Falasdinu da Isra’ila shi ne gimshikin samar da zaman lafiya a yankin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Falasdinawa a matsayin kasa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron   Kan Iyakar Kasashen Biyu

Sojojin kasa na kasashen Iran ta Armenia sun fara atisayen soje na hadin guiwa a tsakaninsu, don kyautata tsaro na kan iyakar kasashen biyu na kuma tsawon kwanaki biyu.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ne suke jagorantar wannan atisayen. Da nufin hana fasa korin muggan kwayoyi da kuma sulalewar yan ta’adda suka kan iyakokin kasashen biyu.

Burgediya Janar Sayyid Mortaza Mira’in babban hafsan  sojojin kasa na IRGC ya bayyana cewa, wannan atisayennn   yana nuna irin yadda sojojin IRGC suke da shirin kare kasar daggga duk wata barazana. Da kuma abota da kyautata makobtaka da kasashe mmmakobta.

Labarin ya kara da cewa ana gudanar da rawan dajin ne a kan kan iyakar kasashen biyu na nordooz.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato
  • Daidaitaccen Tunanin Sin Shi Ne Dabarar Fuskantar Da “Haukar Amurka”
  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 17: Tinubu Ya Kare Yadda Gwamnatinsa Ke Tafiyar Da Tsarin Rabon Arzikin Kasa
  •  Sojojin HKI Sun Yi Kisan Kiyashi A Yankin Shuja’iyya
  • Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron   Kan Iyakar Kasashen Biyu
  • Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
  • Jami’an Amurka da na Saudiyya sun tattauna batutuwan da suka shafi Gaza da yankin