Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet
Published: 10th, April 2025 GMT
Gwamnatin Najeriya ta nuna damuwarta kan yadda masu safarar mutane ke ƙara amfani da kafafen sadarwa na zamani wajen yaudarar mutane da kuma yi musu cin zarafi, inda ta bayyana hakan a matsayin barazana wadda ba ta da iyaka kuma mai saurin yaɗuwa wadda ke buƙatar ɗaukar mataki cikin gaggawa.
Da yake jawabi a taron masu ruwa da tsaki na ƙasa karo na 27 kan safarar mutane da aka gudanar a Abuja a ranar Laraba, Babbar Lauyan Gwamnatin Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi SAN, ya ce dole ne Najeriya ta ɗauki mataki ta hanyar zamani daidai yadda matsalar take saurin faɗaɗa.
Ministan shari’an ya ce, “Safarar mutane ta koma ta intanet. Dole ne mu gaggauta ɗaukar mataki ko kuma mu fuskanci barazanar wuce gona da iri daga masu aikata laifuka waɗanda yanzu suke amfani da manhajoji na zamani wajen samun waɗanda za su yi safara, juya su, da kuma yi musu cin zarafi ta intanet.”
Fagbemi ya bayyana safarar mutane a matsayin sana’ar laifi ta uku mafi samun riba a duniya, bayan safarar miyagun ƙwayoyi da fatauci makamai.
NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma ’Yan bindiga na neman N100m kafin sakin Faston da suka sace a KadunaDaga nan ya yi kira da a ƙara ƙarfin dokoki, hukumomi, da kuma hanyoyin fasahar zamani wajen magance matsalar.
Ya ce, “yaƙi da safarar mutane ba magana ce da ta tsaya kan bayar da alƙaluma ko wasu tsare-tsare ba, batu ne da ke buƙatar a yi a aikace domin tabbatar da adalci da ’yancin walwalar ɗan Adam da kuma kare martabar ƙasa.”
Don haka ya buƙaci kwamishinonin mata a duk jihohin Najeriya su yi ƙoƙarin damar da tsare-tsare da dokoki tare da kafa kwamitocin aiki da cikawa da kuma kasafi da za su taimaka kai-tsaye wajen yaƙar matsalar.
A nata ɓangaren, Babbar Daraktan Hukumar Hana Safarar Mutane ta Kasa (NAPTIP), Binta Adamu Bello, ta bayyana cewa hukumar ta riga ta fara ƙara ƙarfinta a fannin fasahar zamani.
Ta ce, “Yaƙinmu ya koma intanet, kuma martaninmu ma ya koma can,” inda ta bayyana cewa an horar da jami’an tattara bayanai sama da 160 a faɗin ƙasar, yayin da aka kuma ƙaddamar da sabbin manhajoji na zamani domin bibiyar batutuwan safarar ɗan Adam da kuma haɗin gwiwa.
Binta Bello ta ce hukumar ta ceto tare da gyara rayuwar sama da mutane 7,000 tsakanin shekarar 2022 zuwa 2024, kuma an samu nasarar hukunta mutane 205 a cikin wannan lokacin.
Kazalika ta ƙaddamar da jami’an da kai guda 205 domin yaƙi da safarar mutane da kuma cin zarafi a faɗin Najeriya.
Haka kuma ta ƙaddamar da sabbin manhajojin zamani domin inganta tsarin tattara bayanai da kai rahoton safarar ɗan Adam, da haɗin gwiwar Ofishin Majalisar Ɗinkin Duniya mai kula da Muggan Ƙwayoyi da Laifuka (UNODC) da kuma gwamnatin ƙasar Switzerland.
Sauran sun haɗa da farfaɗo da shafin hukumar na kai rahoto da tattara bayanan cin zarafin jinsi, kafa cibiyar zamani a Katsina da kuma farfaɗo da cibiyarta ta zamani a Legas, da gudummawar hukumomin ƙasa da ƙasa irin su ƙungiyoyin ECOWAS, EU da kuma gwamnatin ƙasar Netherlands.
Wakilin UNODC a Najeriya, Cheikh Toure, ya yaba wa ƙoƙarin Najeriya wajen yaƙi da safarar ɗan Adam, inda ya jaddada cewa “manufa ba ta da wani amfani ba tare da aiki a matakin ƙasa ba.”
Ya buƙaci a ƙarfafa dokokin da kuma tsarin tattara bayanai da yanayin kula da waɗanda aka ceto, yana mai jaddada muhimmancin goyon bayan masu ruwa da tsaki a wannan gagarumin aiki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Safarar ɗan Adam safarar ɗan Adam safarar mutane
এছাড়াও পড়ুন:
An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe
Rundunar ’yan sandan Jihar Yobe ta samu gagarumar nasara a ƙoƙarinta na yaƙi da miyagun laifuka, inda ta cafke wasu fitattun mutane biyu da ake zargi da garkuwa da mutane.
Waɗanda aka kama sun haɗa da: Babaro Baushe mai kimanin shekara 40 da Umaru Dau’a, mai kimanin shekara 25 da suka fito daga ƙauyen Askuwari a ƙaramar hukumar Tarmuwa a ranar 9 ga Afrilu, 2025.
Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a KebbiA takardar sanarwar da kakakin rundunar ‘Yan sandan Yobe, SP Dungus Abdulkareem ya fitar ya ce, hedikwatar ’yan sanda reshen Dapchi da misalin ƙarfe 0500hrs, 9 ga Afrilu, 2025, ta cafke waɗanda ake zargin, ’yan ƙungiyar da suka ƙware wajen yin garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa da kuma neman barace-barace, suna gudanar da ayyukansu a ƙananan hukumomin Dapchi da Tarmuwa.
An dai alaƙanta waɗanda ake zargin da laifuka da dama da suka haɗa da: A ranar 21 ga Nuwamba, 2024, masu garkuwar sun kai hari ƙauyen Badegana da kuma kai hari gidan wani da aka kashe, wanda ya yi sanadin rasa rai.
A ranar 10 ga Maris, 2025, waɗanda ake zargin sun karɓe N250,000 da ƙarfi daga Mudi Ibrahim na ƙauyen Askuwari, ƙaramar hukumar Tarmuwa, bayan sun yi barazanar sace shi ko kuma su kashe shi.
Waɗannan mutane sun amsa laifukan da suka aikata, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike a sashin bincike na jihar (SID).
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado ya ba da umarnin ci gaba da ƙoƙarin kama wasu ’yan ƙungiyar kuma ya buƙaci al’umma da su bayar da sahihan bayanai don taimakawa wajen gudanar da bincike.