Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi
Published: 10th, April 2025 GMT
Guguwar ruwan sama ya lalata gidaje da dama a ƙaramar hukumar Shanga ta Jihar Kebbi.
Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris ya jajanta wa al’ummar Garin Kestu da ke unguwar Atuwo a Ƙaramar hukumar Shanga, ya kuma buƙaci iyalan waɗanda abin ya shafa da su ɗauki lamarin a matsayin wata ƙaddara.
Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki a NUPRC — Buba Galadima Matatar Ɗangote ta rage farashin fetur zuwa N865Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labaran gwamnan Ahmed Idris ya fitar.
A cewar sanarwar, gwamnan wanda shugaban Ƙaramar hukumar Shanga, Audu Audu ya wakilta, ya ce ruwan sama mai ƙarfi da ya afku a daren ranar Talata ya lalata gidaje da dukiyoyi na miliyoyin Naira.
Ya kuma tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa, gwamnati za ta bayar da tallafi da suka haɗa da kayayyakin gini.
Gwamnan ya kuma buƙace su da su yi haƙuri, inda ya yi alƙawarin cewa nan ba da daɗewa ba gwamnatin jihar za ta kawo musu ɗauki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ruwan sama
এছাড়াও পড়ুন:
Abubuwa Da Yawa Na Faruwa Ba Tare Da Sanin Tinubu Ba – Tsohon Ma’aikacin Aso Rock
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp