Aminiya:
2025-04-12@21:39:01 GMT

Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta

Published: 10th, April 2025 GMT

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya jagoranci wata tawaga zuwa Jihar Edo domin binciko gaskiyar abin da ya faru game da kisan mafarauta ’yan asalin jihar a ƙauyen Uromi.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ne, ya umarci a kafa wannan tawaga, wacce ta ƙunshi manyan shugabanni irin su Sarkin Rano, Kwamishinonin ma’aikatu da kuma Shugaban Ƙaramar Hukumar Bunkure.

Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki a NUPRC — Buba Galadima

“Manufarmu a bayyane take – bincike, tattaunawa da bayar da shawarwari masu ɗorewa.

“Wannan ba kawai yawon neman gaskiya ba ne, har ila yau ƙoƙari ne na kawo zaman lafiya, domin hana sake faruwar irin wannan tashin hankali,” in ji mataimakin gwamnan

Tawagar za ta gana da Gwamnan Jihar Edo, hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya da ƙungiyoyin fararen hula domin fahimtar matsalar tare da kawo hanyoyin sasanci.

Gwarzo, ya ce tawagar za ta yi duk mai yiwuwa domin ganin an samun zaman lafiya da hana faruwar irin wannan rikici a gaba.

Wannan ƙoƙari na cikin shirin Gwamnonin Arewa na haɗin kai da goyon bayan zaman lafiya a faɗin Najeriya sakamakon ƙaruwar rashin tsaro da ake fuskanta.

“Wannan shiri wani ɓangare ne na matakan haɗin gwiwar Gwamnonin Arewa domin nuna goyon baya, haɗin kai a ƙasa da kuma tunkarar matsalar tsaro da ke ƙaruwa a sassa daban-daban na Najeriya,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo mafarauta mataimakin gwamna

এছাড়াও পড়ুন:

Netanytahu Ya Fusta Da Furucin Kasar Canada Akan Kisan Kiyashi A Gaza

Fira ministan HKI Benjamine Netanyahu ya yi suka cikin fushi saboda Fira ministan kasar Mark Carney  Canada ya bayyana cewa abinda yake faruwa a Falasdinu kisan kiyashi ne.

Shi dai Fira ministan kasar Canada Mark Carney wanda ya halarci taron yankin neman zabe a garin Calgary, yayin da wani daga cikin mahalarta, ya daga murya da karfi yana fada wa Fira ministan cewa, Abinda yake faruwa a Falasdinu kisan kiyashi ne. Shi kuwa Mark Carney ya amsa mas ada cewa; Ina da masaniya, kuma shi ne dalilin da ya sa kasar Canada ta daina sayar wa da Isra’ila makamai.

Sai dai kuma kwana daya bayan abinda ya faru, fira ministan na kasar Canada ya lashe amansa inda ya bayyana cewa, bai ji kamlar kisan kiyashi ba, a cikin abinda aka ambata.

 Wannan bai hana Fira ministan na HKI sukar takwaransa na Canada ba,tare da bayyana shi a matsayin mai kin jinin yuhudawa.

Su kuwa kungiyoyin kare hakkin bil’adama na cikin kasar Canada sun bayyana ja da bayan da Fira minstan ya yi da cewa, ba abinda za a laminta da shi ba ne, ya zama wajibi a gare shi da ya goyi bayan MDD da kungiyoyin kasa da kasa na kare hakkin bil’adama akan cewa; Abinda yake faruwa a Falasdinu kisan kiyashi ne.

Alaka a tsakanin HKI da kuma kasar Canada suna kara kamari,a lokacin da kungiyoyin kasa da kasa suke kara yi wa Tel Aviv matsin lamba akan kawo karshen yakin da take yi a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe
  • An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  • Netanytahu Ya Fusta Da Furucin Kasar Canada Akan Kisan Kiyashi A Gaza
  • Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya
  • NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 10, Sun Kashe Ɗan Bindiga 1 A Katsina