Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron Kan Iyakar Kasashen Biyu
Published: 10th, April 2025 GMT
Sojojin kasa na kasashen Iran ta Armenia sun fara atisayen soje na hadin guiwa a tsakaninsu, don kyautata tsaro na kan iyakar kasashen biyu na kuma tsawon kwanaki biyu.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ne suke jagorantar wannan atisayen.
Burgediya Janar Sayyid Mortaza Mira’in babban hafsan sojojin kasa na IRGC ya bayyana cewa, wannan atisayennn yana nuna irin yadda sojojin IRGC suke da shirin kare kasar daggga duk wata barazana. Da kuma abota da kyautata makobtaka da kasashe mmmakobta.
Labarin ya kara da cewa ana gudanar da rawan dajin ne a kan kan iyakar kasashen biyu na nordooz.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za Ayi Aiki Hadin Gwiwar Tsakanin Efcc Nuj Domin Yaki Da Hako Ma’adanai A Neja
Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) za ta hada gwiwa da kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ) a yaki da hako ma’adinai da kuma ayyukan ta’addanci a kasar nan.
Mukaddashin Daraktan shiyyar Kaduna mai kula da shiyyar Kaduna, Mista Bawa Usman Kaltungo ne ya bayyana hakan a lokacin da ya jagoranci tawagar ofishin shiyya ta Kaduna na EFCC zuwa NUJ a jihar Neja a Minna.
Mista Bawa Usman wanda ya shaida wa manema labarai cewa an kama masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba amma ya ci gaba da cewa “yaki da wadannan laifuffuka ba na EFCC kadai ba ne domin yana da girma da yawa a gare mu don haka yana bukatar hadin kan kowa da kowa.
Ya yabawa ’yan jarida kan kasancewarsu abokan huldar dabarun yaki da cin hanci da rashawa, inda ya jaddada cewa, ayyukan da ake yi a baya-bayan nan kan ayyukan ta’addanci a jihar, shi ne na dakile ayyukan ta’addanci, kuma suna fuskantar shi sosai kuma za mu yi nasara a kan aikin da ke gabanmu.
Mista Musa Bawa Kaltingo ya ce “su (masu aikata laifuka) a yanzu suna kallon jihar Neja a matsayin mafaka kuma suna garzayawa nan don gudanar da ayyukansu.
Da yake mayar da jawabi shugaban majalisar NUJ na jihar Neja, Kwamared Abu Nmodu ya bayyana damuwarsa kan karuwar aikata laifuka ta yanar gizo a jihar Neja, yana mai cewa “abin damuwa ne kuma dole ne mu kawar da duk wani abu mara kyau da ake gani barazana”.
Yayin da yake tabbatar wa EFCC goyon bayan kungiyar, Kwamared Abu Nmodu ya jaddada bukatar hadin gwiwa don tabbatar da cewa an horar da ‘yan jarida kan mafi kyawu a cikin rahoton ayyukan EFCC don samun sakamako mafi kyau.
COV ALIYU LAWAL.