Leadership News Hausa:
2025-04-12@20:57:17 GMT

Waraka Daga Bashin Ketare

Published: 11th, April 2025 GMT

Waraka Daga Bashin Ketare

 

Amfanuwa Da Mamakon Arziki Da A Ka Yi Mana Baiwarsu

Babu shakka, mutuwar zuciya ce ta mai da jama’ar wannan Kasa tamu ta Nijeriya dogara kacokan da sabgar man fetur, a matsayin wata hanya daya tilo da za ta rika samar mana da sama da kashi tamanin ga tattalin arzikinmu na Kasa!. Hakika akwai hanyoyin arzuka iri daban daban cikin wannan Kasa, wadanda ma suka kere fetur sau ninkin ba ninki wajen bunkasar sha’anin tattalin arziki, musamnan sabgar noma, wadda wasu Shekaru can baya, ita ce kashin bayan tattalin arzikin wannan Kasa.

Kuma, tun daga wancan lokaci zuwa yau din, harkar noma ce kan gaban fetur, wajen samawa dubban jama’ar Kasa aiyukan-yi.

Yankin arewacin wannan Kasa ta Nijeriya, na daga wuraren da suka fi ko’ina a Duniya kyawon kasar noma. Yankin na arewa, ya fi ko’ina a yankin Afurka ta yamma (West Africa) yawan matattarar ruwa, ko a ce dam dam, wanda ake amfani da su wajen noman rani. Ga dandazon albarkar jama’a da Allah Ya ba mu, wadanda za su wadata wajen noma irin wadannan kyawawan kassai da aka yi mana baiwarsu. Bangaren noman ne ke samawa dubban jama’ar yankin aiyukan-yi sama da komai a ban Kasa, sai dai, shugabanni sun gaza shigowa bangaren na noma, don inganta shi ingantawa.

A Kasar Amurka, Kasar da shugabanni suka shiga harkar tallafar noma kan-jiki kan karfi, ta tabbata cewa, kudin shigar da lemon zaki “Orange” kawai ke samawa Kasar a Shekara, ya fi kudin shigar da gwamnatin Nijeriya ke samu a Shekara wajen man fetur!. Ita kanta Amurkar, ba za ta fada mana ni’imar albarkatun kasa ba, amma sai ga su sun fi mu amfanarsu. Me ya sa? Amsa, shugabanninsu da gaske ne suke, a yunkurinsu na inganta tattalin arzikin Kasar.

Iskar gas kawai da Allah Yai wa Nijeriya baiwarsa, zai iya daukar nauyin bai wa daukacin nahiyar Afurka da ke kunshe da Kasashe 52 ko 53 wajen sama musu wadatacciyar iskar gas. To Amma dan Nijeriya a yau, nawa ne yake shan litar gas? Da kuma mai karatu zai lalubi wasu Kasashe cikin Duniya da ko kama kafarmu ba su yi ba wajen mallakar iskar gas din, sai ya samu kuma sun fi mu shan gas din da arha!. Wadanne irin shugabanni muke da su ne? Eh mana, tun da sarrafawa da inganta harkar gas din, na hannunsu ne.

Misali mutum ya ce fetur, gas, rake, lemo da makamantansu, za a ga an ba mu albarkatun kasa na abubuwa daidai har sama dari biyu da hamsin (250) iri daban daban. Cikin wadannan albarkatun kasa akwai bishiyar Katako, wani masani ke cewa, da Nijeriya za ta inganta bishiyoyin Katako da take da su, su kadai, za su iya zama abin dogara kamar man fetur, kuma su rike Kasar. Wane shiri ne a kasa a yau da mutanen wannan Kasa za su ce sun ga gwamnati na yi, don inganta sabgar bishiyoyin Katakonta?

Mutum ya dauki gyada kawai, zai yi matukar mamakin irin tattalin arzikin da ke kunshe cikinta. Daga gyada, akwai sinadaran da ake yin sabulu, abin yin biskit, abin yin abincin dabbobi, abincin kifi, abincin kaji da sauransu. Ka da mai karatu ya mance da man girki da ake samu daga gyadar. Ko mai karatu ya san da cewa a na yin makarin inji daga matsanancin hucin zafi, wanda a turance ake kira da “engine gasket” da bawon gyadar? To amma a yau, wane hobasa ne na hakika ba na baka ba, da za a ce gwamnatocinmu na yi, don ganin mun amfana hakikar amfanuwa daga mamakon tattalin arziki da ke kunshe cikin gyada?

Cikin wata budaddiyar wasika da Dattijo, Alhaji Dattijo Adhama ya rubuta zuwa ga hukumomi masu gudanarwa da masu yin doka na arewacin wannan kasar, “An Open Letter To The Northan Edecutibes & Legislatures” a Watan Yulin Shekarar 2021 (July, 2021), da mutum zai duba shafi na biyar (P5) na wannan wasika, zai amfana da wata irin kididdiga da aka yi, wadda ta nuna irin biliyoyin kudaden da jihar Kano za ta iya samu a kullum daga man gyadar da za a sha a cikin jihar. Cikin kididdigar, an nuna cewa, jihar ta Kano na iya samun kudin shiga sama da naira biliyan saba’in da biyu (N72b) a kullum. Da sharadin, wancan bangare na masu zartarwa da masu doka sun shigo sun gama kai wajeguda, tare da datse shigowar man gyadar daga Kasashen ketare, ta hanyar yin doka a Majalisa.

A tsakanin garin Makoda da Dambatta, akwai wani nau’in yashi da Kasar China ke ta begen ganin ta sami kai wa ga tononsa, don sana’anta gilashi da shi. Duk cikar Kasar ta China, ba su da wani ma’adin yin gilashi sama da irin wannan yashi na tsakanin Dambatta da Makoda. Idan ban manta ba, wani lokaci can baya, ta hanyar Malam Gambo, shugaban ma’aikata “Staff Officer” na Kasuwar Sabon Gari, ya gabatar min da shugabancin masu harkar gilashi ta Kasuwar Kofar Ruwa, na wuce gaba zuwa kai kuka ga Sanatan yankin, Barau Jibril”, da zimmar ya wuce musu gaba wajen tono yashin, amma lamarin ya gagari kundila.

Ba sai Kano ba, muddin mai karatu dan Nijeriya ne, ba zai gaza tunanin wani ma’adin ko albarkar Kasa da Allah Ya hore musu a yankinsu ba. Babbar matsalar a yau ita ce, masu mulki ba su damu da hako ko amfanar da jama’ar Kasa daga irin wadancan amfanoni da Allah Yai mana baiwarsu ba. Sai ma aka wayigari, idan akwai wani ma’adani a waje, sai a sami wasu marasa kishin kasa su game baki da Turawa, a zo a haddasa mummunar fitinar da za ta kai ga kashe rayukan dubban jama’a a wajen. Bayan kowa ya yi kaura ya yi gudun tsira da ransa, sai wadancan marasa kishin kasa da bakin haure su dukufa kwasar wadancan ma’adanai, shin, me ke faruwa a Zamfara a yau?

Duk irin albarkatun kasa da aka yi wa wata Kasa baiwarsa a Duniya, muddin shugabanninta ba sa kishinta, to fa a banza, ba za su amfana ba. Kuma ba za a bar su su zauna lafiya ba.

Da shugabanni a Nijeriya za su karkata ga sabgar noma kadai, su zuba jari ciki, su samawa manoman taki da kasuwa, babu shakka da an fita daga wannan kagaggen talaucin da aka jefa jama’ar wannan Kasa ciki. Talaucin Kasar Nijeriya ba daga ne yake ba, tun da Allahn Ya ba da mafita.

 

Samar Da Gungun Masana Masu Kishin Kasa

Dole ne gwamnati ta yi zabarin manyan mutane masana gogaggu, wadanda lamarin Kasar ne ke kunshe cikin zukatansu sabanin muradansu na son zuciya. Hakika Allah Yai mana baiwar mutane hazikai masana, wadanda hatta sassan Kasashen Duniya ke daukarsu aikin dindindin da na kwantaragi, don inganta harkokin Kasashen nasu. Dole ne a lalube su, a saurari shawarwarinsu, a dabbaka abubuwan da za su gabatar a matsayin shawara ko a matsayin wani sharadin da wajibi ne binsa, wajen inganta harkokin tattalin arzikin namu, muddin a na son A’i ta fita daga rogo ba tare da ta karce jiki ba.

Lokacin da marigayi Umar Musa ‘yar’adua ya tasamma yin gyara game da sha’anin Zabe a Nijeriya, ya kafa wani babban Kwamiti ne a karkashin tsohon babban Joji na Kasa Uwaisu, da sauran masu kishin kasa, mutane irinsu Farfesa Attahiru Muhammad Jega, OFR, ai sanin kowane cewa, a karshe, laya ta yi kyawon rufi. Gwamnati ba ta yi wa kwamitin wani katsa-landan ba, sannan kuma ta tasamma dabbaka irin shawarwarin da wancan kwamitin ya gabatar mata. Bugu da kari, gwamnati ta dauko guda daga cikin ‘yan kwamitin, Jega, ta danka hukumar zaben Kasar kacokan a hannunsa, hakan ne ya jaza aiwatar da zabukan da ba a taba samun masu ingancinsu ba cikin tarihin Zabukan Kasar gabaninsu, wato Zabukan Shekarun 2011 da na 2015, kamar yadda masana da sauran masu sanya idanu na gida da waje suka fadi.

Ko da an kafa wani kwamiti na masana kuma masu kishin kasar, muddin za a yi musu katsa-landan cikin sabgar kwamitin, ko kuwa, shawarwarin da suka gabatar, a yi wurgi da su, to fa babu inda za a je, sai dai kawai a ci gaba ne da tsalle a wajeguda kamar yadda aka saba.

Duk kyawon wani kwamiti da sunan gyara tattalin arzikin Kasa da aka kafa, ko za a kafa ba bisa cikakkiyar cancanta ba, shi ma ba zai cimma komai ba mai alfanu, lamura za su ci gaba da wakana ne cikin yanayi na daben-kwalo.

Duk karatu da Dr Abel Guobadia da Professor Maurice Iwu ke da, ba su jagorantar Hukumar Zabe, INEC, ta Kasa da aka yi bisa wata manufa, a karshen lamarin, sun gudanar da wasu nau’ikan Zabuka ne gurbatattu, wadanda gabaninsu a Kasar, ba a taba cin karo da miyagun Zabukan irinsu ba!.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ketare

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Masu Shirin Yin Kawance Na Duba Yiwuwar Zakulo Dan Takarar Da Zai Yi Wa’adi Daya

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku ya kasance mai fafutukar tabbatar da hadin kan ‘yan adawa, yana mai jaddada muhimmancin hadin gwiwa wajen kayar da Tinubu a zaben 2027.

A ranar 8 ga watan Maris ne ya bayyana kokarinsa na hada kan ‘yan adawa da kafa kawancen korar jam’iyyar APC.

Bayan sauya shekar El-Rufa’i daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PSP a ranar 10 ga watan Maris, tattaunawar da aka yi tsakanin shugabannin ‘yan adawa ta samu gagarumar nasara.

Atiku da sauran ‘yan adawa sun bayyana cewa taron na ranar 20 ga watan Maris ya nuna kaddamar da kawancen a hukumance.

A baya dai an ruwaito a ranar 23 ga watan Maris cewa ana jinkirin tattaunawa kawance tsakanin shugabannin siyasa saboda burin tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku na tsayawa takara da kuma rikicin shiyya.

Majiya ta bayyana cewa masu ruwa da tsaki suna da zabi da yawa don magance duk abubuwan da lamarin ya kunsa.

Majiyar ta ce, “Akwai batutuwa da dama a tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki a tattaunawar kawancen, inda batun arewa da kudu shi ne babban abin da ya fi daukar hankali.

“Yawancinmu mun fahimci cewa idan muka tsayar da dan takarar kudu wanda ya cancanta kuma mai gaskiya, kayar da Shugaba Tinubu zai fi sauki. Don haka da yawa daga cikin masu ruwa da tsaki, musamman na arewa, suna kira ga Atiku a kan kar ya tsaya takara, ya bai wa kawancen damar mara wa dan takarar kudancin kasar nan baya da zai yi wa’adi daya idan aka zabe shi.

“A hakika, wasu daga cikin wadannan masu ruwa da tsaki sun dagewa cewa duk wani dan takara daga kudu da za su mara masa baya dole ne ya amince da alkawarin wa’adi daya.

“Wadannan al’amura sun kunno kai, amma mun himmatu wajen magance su a lokacin da suka taso da kuma daukar nauyin ‘yan Nijeriya da dama da suke fuskantar rashin iya shugabancin APC. Manufarmu ita ce tabbatar da ingantaccen tsari wanda ke wakiltar muradun jama’a da karfafa hadin kan kawancen.”

A lokacin da aka yi yunkurin jin ta bakinsa, sakataren kungiyar hadin kan jam’iyyun siyasa ta kasa, Peter Ahmeh, ya tabbatar da cewa masu ruwa da tsaki na yin la’akari da shawarar fitar da dan takara daga kudancin kasar nan tare rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta wa’adi guda.

Ahmeh ya bayyana cewa, kawancen ‘yan adawar da ke adawa da Shugaba Tinubu sun fi wadanda tsohon shugaban kasar Goodluck Jonathan ya fuskanta a shekarar 2014.

Ya ce, “Rattaba hannu kan yarjejeniyar wa’adi guda da dan takara daga kudu na daga cikin abin da ke kan teburin tattauwar, amma har yanzu ba a kammala hakan ba. Bai kai ga karshe ba.

“Peter Obi da wasu masu neman takar shugaban kasa a kudu suka cikin wannan tattaunawa. Na yi imanin cewa za a cimma matsaya nan da ‘yan makonni masu zuwa.

“Akwai zabi masu yawa a kan tebur. Mutane suna kawo sauye-sauye daban-daban, amma gaskiya har yanzu ba a cimma matsaya ba. Da zaran an cimma matsaya kan wannan yarjejeniyar, za mu sanar da al’umma.

“A bayyane yake cewa ‘yan Nijeriya da yawa sun fahimci cewa wannan gwamnati tana cutar da mu fiye da alherinta. Don haka, ‘yan Nijeriya da dama ne ke shiga kawancen. Akwai ‘yan adawa da ke adawa da wannan gwamnati fiye da yadda ake yi wa tsohon shugaban kasar Jonathan a shekarar 2014.

“Don haka, ina kira ga dukkan masu ruwa da tsaki na kkwancen da sauran shugabannin ‘yan adawa da su ci gaba da wannan alkawari domin mu hada kai don ceto kasar nan daga gazawar APC.”

Lokacin da aka tuntubi tsohon mataimakin shugaban kasar, Atiku kai ji ta bakinsa kan wannan kawance, ya yi gargadi game da rade-radin da ka iya kawo cikas ga tattaunawar kawancen.

Atiku, ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya jaddada cewa duk wata yarjejeniya da aka kulla za ta kasance wajibi ga dukkan bangarorin da abin ya shafa.

Shugaban jam’iyyar SDP na kasa, Shehu Gabam ya tabbatar da cewa ana ci gaba da tuntubar juna a fadin kasar nan kan wannan kawancen ‘yan adawa.

Sai dai kuma shugaban matasan jam’iyyar PDP, Timothy Osadolor, ya soki yunkurin da ake yi na dan kudu ya rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta wa’adi daya, yana mai cewa lamarin ba mai yiwuwa ba ne.

Da yake mayar da martani kan kawancen ‘yan adawa, Daraktan Yada Labarai na APC, Bala Ibrahim, ya yi watsi da yunkurin kawancen, inda ya bayyana cewa farin jinin jam’iyya mai mulki a tsakanin ‘yan Nijeriya na karuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13
  • 2027: Masu Shirin Yin Kawance Na Duba Yiwuwar Zakulo Dan Takarar Da Zai Yi Wa’adi Daya
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 17: Tinubu Ya Kare Yadda Gwamnatinsa Ke Tafiyar Da Tsarin Rabon Arzikin Kasa
  • Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta