’Yan bindiga sun harbe mata 2 a gona a Kogi
Published: 11th, April 2025 GMT
Wasu mahara sun harbe wasu mata biyu har lahira tare da banka musu wuta a gonakinsu da ke ƙauyen Okete a Ƙaramar Hukumar Dekina ta Jihar Kogi.
Lamarin ya faru ne a lokacin da kowacce daga cikin matan biyu ke tsaka da kula gonarta.
An ce maharan sun yi musu ruwan harsasai baya wata taƙaddama da ta ɓarke, sannan suka tsere zuwa wani wuri da ba a sani ba.
Wani mazaunin yankin ya ce, “Muna cikin juyayi tun da muka samu labarin harin da aka kai wa ’ya’yanmu mata a gona. Sun je gonakinsu ne domin su kula da su a ranar Laraba, abin takaici sai wata ta ƙaddamanta ɓarke, kuma maharan, waɗanda ake zargin makiyaya ne, suka harbe su har lahira.
“Mun yi tunanin za mu ɗauko su da rai ne lokacin da muka samu labarin a ranar Laraba, amma sai muka iske gawarwakinsu an yi musu ruwan harsasai da kuma ƙuna a jikinsu.”
Cutar Kwastomomi: NERC ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar N628m ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Nejaউৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
Mata a Jihar Jigawa sun yi kira da gwamnati da kungiyoyin agaji masu zaman kansu da su samar da magungunan samun tazarar haihuwa kyauta domin inganta tsarin iyali.
Matan da suka tattauna da wakilinmu a cibiyoyin kula da lafiya na Kudai da Kachi dake Dutse, a yayin bikin ranar Lafiyar Uwa ta duniya, wato “Safe Motherhood” a turance, sun bayyana damuwarsu kan rashin samuwar kayayyakin bada tazarar haihuwa.
Wata uwa mai yara uku, Malama Karimatu Sani, ta ce duk lokacin da ta je siyan maganin samar da tazarar haihuwa, ana bata wadanda lokacin aikinsu ya wuce, wanda hakan na iya haifar da illa ga lafiyar mata.
“Sau da dama sai na jira asibiti ya samu sababbin kaya, ina addu’ar kada na samu ciki kafin a kawo wadannan magunguna da ake badawa kyauta.” in ji ta.
Wata mai suna Maryam Abubakar, ta bayyana cewa tana kashe kudi masu yawa wajen zuwa asibiti don dubawa ko kayan sun samu.
Ta koka da cewa siyan kayan bada tazarar haihuwa daga shagunan magani a waje yana da tsada sosai wanda hakan yana hana mata damar siya.
A madadin mata na jihar, ta yi kira ga gwamnati da kungiyoyin agaji da su kawo musu dauki domin mutane da dama suna rungumar tsarin tsara iyali a matsayin mafita ga matsalolin da ke damun al’umma.
A gefe guda, wata ma’aikaciyar lafiya a cibiyar kula da lafiya ta Kachi, Amina Sulaiman, ta tabbatar da cewa kayayyakin samar da tazarar haihuwa sun kare a asibitin tun watanni biyu da suka wuce.
“Muna takaicin yadda mata sukan zo don yin tsarin iyali amma babu biyan bukata saboda rashin kayan aiki da magunguna”.
Hajiya Amina Sulaiman ta yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da ssusamar da kayayyakin don ragewa mata radadin rayuwa.
A bara ne gwamnatin jihar Jigawa ta kaddamar da kwamiti mai mambobi ashirin da uku kan Lafiyar Uwa, da ke da alhakin farfado da hanyoyin kula da lafiyar uwa a jihar.
Sakataren gwamnatin jihar, Malam Bala Ibrahim, yayin kaddamar da kwamitin a ofishinsa, ya bayyana cewa aikin kwamitin ya hada da duba yadda ake aiwatar da shirin Lafiyar Uwa da kirkirar tsarin aiwatarwa domin karfafa abinci mai gina jiki da shawarwari don samun kulawa da uwa da jarirai.
Sauran ayyukan sun hada da yin bincike kan yadda shirin ke gudana da kirkirar hanyoyi don karfafa tura mata zuwa cibiyoyin lafiya daga cikin al’umma.
Yayin kaddamar da kwamitin, Malam Bala Ibrahim ya kara da cewa an fara aiwatar da shirin ne a shekarar 2006 karkashin shirin tallafin na DFID.
Ya ce daya daga cikin muhimman sassa na shirin shi ne tsarin daukar gaggawa, inda aka samar da motoci don daukar mata masu nakuda zuwa cibiyar lafiya mafi kusa don samun ingantacciyar kulawa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, maza da mata da dama daga yankunan karkara a jihar Jigawa sun rungumi tsarin bada tazarar haihuwa da shirin Lafiyar Uwa, suna kuma cin moriyar su ta bangaren lafiya da tattalin arziki.
Usman Mohammed Zaria