Wani jirgi mai saukar ungulu ya faɗa cikin kogin Hudson da ke birnin New York a Amurka.

 

Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun bayyana cewa mutum shida da ke cikin jirgin – fasinja biyar da direban jirgi guda sun mutu.

 

Magajin garin New York Eric Adams ya ce jirgin na ɗauke da wani iyali su biyar daga Spain har da yara uku.

 

Ya ƙara da cewa tuni aka tsamo gawarwakin mutum biyar ɗin daga ruwa.

 

Wakilin BBC ya ce har yanzu ana aikin ceto domin koƙarin zaƙulo tarkacen jirgin da masu bincike za su buƙata don gano abin da ya haddasa haɗarin.

 

Shaidu sun ce jirgin ya tarwatse ne tun a sama inda kuma ya faɗa cikin kogin.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hadari

এছাড়াও পড়ুন:

Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza

Kafar watsa labaru ta ” Axio ta Amurka ta watsa wani rahoto da yake nuni da cewa, an sami rashin yarda da juna a tsakanin masu zuba hannun jari na kasa da kasa da kuma Amurka.

Kafar watsa labaran ta buga a shafinta na “Internet” cewa; Rashin tabbaci da yake faruwa a halin yanzu a cikin kasuwanni  yana  tsoratar da masu zuba hannun jari a duniya.

Rahoton ya kuma ambaci girgizar da Dalar Amurka take yi, da kuma muhimman takardun da suke a matsayin kaddara a cikin Baitul-malin Amurka.

Kafar watsa labarun ta ce, a baya muhimman takardun da suke a matsayin kaddara a cikin Baitul-malin Amurka, wadanda kuma su ne ke bai wa Dalar Amurka kariya, sun kasance masu karfafa gwiwar masu zuba hannun jari, amma daga makon da ya shude an sami rashin aminci.

Abinda ya faru a makon da ya shude kamar yadda kafar watsa labarun ta ambata yana a matsayin karaurawar hatsari da aka kada, a tsakanin wadanda su ka yi Imani da tsarin kudade da Amurka take jagoranta, tun bayan kawo karshen yakin duniya da biyu.

Haka nan kuma ta yi ishara da cewa a lokacin da aka sami matsalar tattalin arziki a duniya a 2008, da kuma bullar cutar corona a 2020, Dalar Amurka ta rika habaka da tashi sama,amma yanzu akasin haka ne yake faruwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
  • Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi
  • An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi 
  • ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja
  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China