UBEC Ta Bayyana Jihar Jigawa A Matsayin Abin Kuyi A Fannin Ilimi
Published: 11th, April 2025 GMT
Hukumar ilimin bai daya ta kasa wato UBEC ta yabawa Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa bisa jajircewar sa wajen inganta ilimi a matakin farko a Jihar.
Shugabar Hukumar, Hajiya Aisha Garba, ta bayyana hakan a yayin ziyarar gwamnan zuwa hedikwatar UBEC a Abuja.
Hajiya Aisha Garba ta bayyana jihar Jigawa a matsayin abin koyi ga sauran jihohin kasar nan.
Kazalika, ta jaddada irin yadda gwamnati ta zage damtse wajen zuba jari a harkar ilmi, tana mai cewa Jihar ta karɓi fiye da Naira biliyan 21 daga tallafin UBEC tun daga shekarar 2004, wanda ya sanya ta cikin jihohin da suka fi cika sharudan samun tallafin UBEC.
Ta kuma lissafa wasu daga cikin nasarorin da aka cimma a ƙarƙashin Gwamna Namadi wadanda suka hada da gina fiye da ajujuwa 3,000 da rijiyoyi 500 da daukar malaman makaranta fiye da 7,000.
Tace Gwamnatin ta kuma horas da malamai sama da 17,000 da kaddamar da Kungiyoyin Iyaye Mata da Ƙarfafa Kwamitocin Gudanarwar Makarantu wato SBMC da kuma kulla haɗin gwiwa da wani kamfani a shirin Jigawa UNITES.
A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya jaddada cewar, gwamnatin sa ta himmatu wajen sauya tsarin karatu da inganta sakamako ta hanyar amfani da bayanai da kuma haɗa kai da al’umma.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Sama Da 240 A Kebbi
Sama da gidaje dari biyu da arba’in ne aka lalata a daren Talatar da ta gabata, ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka shafe sa’o’i ana yi a unguwar Garin Kestu Atuwo dake karamar hukumar Shanga ta jihar Kebbi.
Da yake jajantawa wadanda abin ya shafa, Gwamna Nasir Idris ya shawarci gidajen da abin ya shafa da su dauki lamarin a matsayin wani kaddara daga Allah Ta’ala.
Shugaban karamar hukumar Shanga, Alhaji Audu Dan Audu, ya wakilce shi, ya ce ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi a daren ranar Talata ya lalata gidaje da dukiyoyi na miliyoyin Naira, ya kuma yi godiya ga Allah Madaukakin Sarki ganin yadda ba a yi asarar rayuka ba.
Ya kuma yi kira gare su da su yi hakuri domin nan bada jimawa gwamnatin jihar za ta mika musu tallafi da suka hada da kayayyakin gini.
Abdullahi Tukur