Ba kamar kayayyakin manyan kamfanoni irin su Ajinomoto, Bedan wadanda aka zuba su a cikin kwali, ana sayar da su cikin lafiyayyen mazubi kuma NAFDAC ta amince da su ba, wadannan danyun kaya ne da ba su da wata alama.

Babban abin ban tsoro shi ne ba za a iya gano masana’antunsu don bincikar sahihancinsu ba.

Da alama a yankin Arewacin Nijeriya din ake yin su amma an gaza gano hakan ko kuma an gano amma wa’alla saboda yawan bukatu an kasa dakilewa.

Bincike ya nuna cewa a kasuwar Singer da Abubakar Rimi da ke Kano, ana sayar da buhu mai nauyin kilo giram 25 na wannan sinadari kan Naira 45,000, wanda ke bai wa ‘yan kasuwa damar sayar da su a kanana wurare, ciki har da auna shi da abin da mazauna yankin ke kira ‘mudu’.

A manyan kasuwannin Kaduna da Maiduguri, kasuwar Sabon Gari da ke Sokoto, ana sayar da buhu mai nauyin kilogiram 25 a tsakanin Naira 46,000 zuwa Naira 50,000.

A cikin jaka mai nauyin kilo giram 25, ana iya samun kamar mudu ‘10 zuwa 15 ‘.

Abokan ciniki, ba tare da la’akari da hadarin dake tattare da kiwon lafiya ba, sun fi son wannan haramtaccen samfuri saboda yawan abin da za su samu daga mudu da kuma saukin yin almundahana ta hanyar cakuda shi da gishiri don kara yawansa da samun riba.

A kwanakin baya ne hukumar ta NAFDAC ta rufe wani dakin ajiyar kaya na kamfanin ‘DEE-LITE IMPED Distribution Co. Ltd’ da ke Jihar Sokoto, bayan ta gano wani adadi mai yawa na kayan abinci marasa rajista da suka hada da buhu 5,347 na MSG.

Rumbun ajiyar da ke kan titin Coca-Cola, daura da Western Bypass a Sokoto, an gano ya saba wa ka’idojin hukumar NAFDAC. A cewar hukumar ta NAFDAC, kamfanin ya shigo da haramtaccen samfurin MSG babu izini a karkashin takardar izinin sarrafawa amma an same shi yana sayar da samfurin kai tsaye, wanda haramun ne kuma yana da hadari ga lafiyar dan’Adam.

Wani masani kan harkokin kiwon lafiya da ke zaune a Gombe, Dokta Abdullahi Guruji ya ce ya kamata masu amfani da su su yi hattara da abubuwan da suke amfani da su domin gujewa duk wata matsala a fannin lafiya. Guruji ya ce ya zama wajibi masu amfani da su daina sadaukar da lafiyarsu a kan burin farashin kayan abinci masu arha.

A cewarsa, bai kamata a ce alhakin kare lafiyar mutum ya takaita ga hukumar NAFDAC da SON da sauran hukumomi kadai ba. Ya bukaci kowane dan Nijeriya da ya kula da kansa da kuma sauran ‘yan kasarsa domin kaucewa wannan hatsarin da ke kunno kai a harkar lafiya.

A yayin da yake kira ga masu sayar da abinci da su taka rawar gani a wannan fanni, ya bukace su da su kula da lafiyar kwastomominsu ta hanyar yin amfani da ingantattun kayayyakin dafa abinci.

Sai dai kwarare a fannin lafiyar ya dora wa hukumar ta NAFDAC alhakin kara kaimi a fannin tabbatar da doka da oda inda ya ce yin hakan zai dakile ayyukan marasa kishin Nijeriya da suke jajircewa wajen cutar da ‘yan Nijeriya.

“Duk lokacin da muka ziyarci kasuwa, za mu ceci mutane da yawa daga matsalolin kiwon lafiya ta hanyar rufe shagunan masu sayar da monosodium glutamate, masu sayar da magungunan jabu / marasa inganci, da masu siyar da abubuwan sha masu dandano, na cikin kwalba a cikin sauran abubuwan da ke zama abin sha,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Hadari Kasuwanni Lafiya ana sayar da

এছাড়াও পড়ুন:

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

 

-Mun lura da ilimomin harkokin zamaninmu a cikin Alkur’ani

Cikin godiyar Allah, muna mika ziyara ga Shehu Isma’ila Umar Almadda (Mai Diwani) da kuma ban gajiya da gabatar da Tafsirin Alkur’ani mai girma na Azumin Ramadan na bana. Allah ya kai mu na badi albarkar Annabi (SAW) da Shehu (RTA).

Ya Shehi, a Tafsirinka na rana ta bakwai mun ji yadda ka yi bayani na ilimomin kiyaye hadurran hanya da ke kunshe a cikin aya ta 63 ta Suratul Furkan (Sura ta 25), “Wa Ibadur Rahman…”.

Mun kara fahimtar cewa, ayar tana nusarwa a kan tafiya cikin tsari walau sufuri ne na titin mota, ko na jirgin sama ko na ruwa ko jirgin kasa, da dukkan alamomin da ake sakawa na gane hanya da kiyaye aukuwar hadurra na ganganci da sauran ilimomin da suka kunshi dokokin hanya, duka suna nan a karkashin fahimtar ayar. Allah ya saka da alkhairi.

Game da sunan Allah na “Arrahmanu” kuwa, ya kara nuna mana cewa ya kunshi kowane ilimi. Kuma duk masana na sunan na “Arrahmanu” su ne suke zama kwararru na kowane fanni da ke tafiya a kan kasa cikin ilimi da kwarewa. Wallahi, wannan yana nuna mana cewa, mu al’umma musamman ta musulmi mu dage da neman ilimi na kowane fanni saboda inganta rayuwa da aiki da ilimin wajen nuna sanin ya kamata.

Daga misalan da ka kawo na batun hanya, na fahimci cewa, idan alamar hanya ta jar danja ta tsayar da direba shi kuma ya ki tsayawa, ya nuna jahilci ko rashin aiki da ilimin, wanda hakan ne yake sa jami’an da abin ya shafa suke hukunta direbobi masu karya dokokin hanya. Su kuma jami’an, yadda suke fara tambayar mai laifin a game da shin yana da lasisin tuki domin tantance cewa, shi a cikin “Ibadur Rahman” yake ko kuma jahili ne. Idan jahili ne hukuncinsa daban, idan kuma wanda ya san abin ne, watau yana daga cikin “Ibadur Rahman”, har yana da lasisi to hukuncinsa ma yakan fi tsanani, duka ya fahimtar da mu cewa muna da komai a cikin Alkur’ani.

Allah ya saka maka da alheri bisa yadda kuma ka karfafa gwiwar masu mulki har ma da magidanta a kan koyar da duk wadanda suke karkashinsu ilimi, domin tabbas jahilci tamkar mutuwa yake. Idan an ba mutane ilimi shi ne zai zama an raya su, haka nan idan an bar su da jahilci to kuma babu makawa an kashe su.

Muna godiya ya Shehi, Allah ya kara lafiya da nisan kwana.

 

-Tabbas Ya Kamata Mu Zurfafa Bincikenmu A Cikin Alkur’ani Domin Samun Ci Gaba

Assalamu alaikum. Ya Sayyadi barkanmu da kammala watan Azumin Ramadan, Allah ya amsa ibadunmu ya sa muna cikin ‘yantattun da aka ‘yantar, amin. Hakika bayanin da ka yi a kan yadda ya kamata mu al’ummar musulmi mu kara zurfafa bincike a cikin Alkur’ani domin samar da ci gaban zamani da ake gani a ko ina cikin duniya babban lamari ne mai matukar muhimmanci da ya kamata kasashenmu na musulmi mu mayar da hankali a kai.

Musamman ma, mu kasashen Afirka da muka zama koma baya idan aka kwatanta da sauran yankuna na duniya, ya kamata mu su sake nazarin wayewar zamani da ke kunshe cikin Alkur’ani, wanda hakan zai sanya mu iya yin kafada-da-kafada da manyan kasashen duniya irin su Amurka da China ta fannin ci gaban zamani.

Duk wanda ya san tarihi da kuma ilimi, ya san cewa duk bayanan da wadannan kasashen da suka ci gaba suke takama da su da kundayen da suka mallaka na bayanan ilimi muna nan da su a cikin Alkur’ani, abin da ya kamata a yi shi ne mu fadada bincike na fahimtar zamani a cikin Alkur’ani wanda hakan zai bai wa mu Afirka damar yin kirkire-kirkire da gudanar da sabbin ayyuka na ci gaban zamani.

Yana da kyau yadda muke da yawan mahaddata a Nijeriya, ya zama kasar ta zamo kan gaba wajen zama abar koyi a fannin kawo ci gaban zamani a Afirka da kuma inganta rayuwar ‘yan Afirka. Muna da yakinin cewa, in dai an sa hakan a gaba, tabbas nan da shekaru masu zuwa za mu iya cimma duk burin da muke so mu ga mun cimmawa.

Kuma har ila yau, mun ji dadi a kan kiran da ka yi na a sake nazarin wasu abubuwa na shari’a da ba su da asali a ainihin nassin da Allah ya saukar, domin tabbas abubuwan da Allah ya haramta da hukuncinsa (Muharramatu) kuma ya kulle su da hukunce-hukunce (Muhkamatu) babu wanda ya isa ya kara ko ya rage, kuma Allah bai bar su a dunkule ba, ya yi bayaninsu dalla-dalla.

Yadda aka fara shigo da abubuwa cikin addinin nan tun daga zamanin Sahabbai ya rikita abubuwa da yawa. Wannan ba rashin kunya ba ne ko kadan, muna girmama dukkan Sahabbai wallahi, kuma a cikinsu ne wasu suka tsawatar a kan shigo da abubuwa cikin addinin. Ga misalin Hadisin Ka’abu bin Malik, lokacin da wasu matasa suka ziyarce shi, suka yi masa kirarin girmamawa, suka bukaci ya yi musu hira daga cikin rayuwarsa tare da Annabi (SAW), wanda ya ce, musu “in kun ji na yi shiru ku ma ku yi shiru, yadda kaina ya yi fari (furfura) haka kwakwalwata ta yi, kuma abubuwa ne na yadda muka yi rayuwa da Rasulullahi (SAW). Bari na fada muku duk sai da aka canja su face Sallah (kadai), ita ma ga ta nan kun fara canzawa”. Duk wannan ya nuna cewa, ya kamata mu dawo kan turba ta asali.

Allah ya saka da alkhairi, ya Sayyadi. Wallahi muna godiya sosai, domin mun kuma karu da bayanai a kan abubuwan da Shari’a ke kewayawa a kansu na batun da ya shafi daukar kudi daga nan zuwa nan kamar rabon gado; da tsara Iyali da yadda za a yi aure da rabuwarsa da yadda za a yi tarayya a cikin dangi; da ukuba da hukunci a tsakanin abokan hulda. Haka nan, sauran harkoki irin su kokarin tabbatar da zaman lafiya wanda ya kunshi yadda ake shirya yaki, da sulhu, da zaman lumana; da batun riba da ke bayani a kan tsarin yadda za a gudanar da kasuwanci, sai kuma abubuwan da suka shafi dabi’o’i na ‘yan’adam.

Hakika duk sauran abubuwan da ba wadannan ba, Shari’a ta bar mutane su yi hukunci da abin da ke zamaninsu, na daga kundin tsarin mulki da ake shimfidawa don maslahar al’umma wajen habaka tattalin arziki da raya kasa.

Allah ya kara ilimi da fahimta a cikin wannan addini mai fadi da Manzon Rahama, Annabi (SAW) ya zo mana da shi domin tseratar da al’umma duka sai dai wanda ya ki. Mun gode.

Sako daga Malam Miftahu Adam Zariya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Ba Matan Arewa Ta Gabas Su Dubu Tallafin Naira Miliyan 50
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  • Gwamnati ta gargaɗi jihohi 30 kan ambaliyar ruwa