Aminiya:
2025-04-12@21:11:32 GMT

An saki fasto an kuma tsare wanda ya kai kuɗin fansa

Published: 11th, April 2025 GMT

’Yan bindigan da suka sace Fasto Samson Ndah Ali na cocin ECWA da ke Mararaba Aboro a Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna, sun sake shi sannan sun tsare wanda ya kai kuɗin fansar, Yusuf Shehu Ambi, wanda shi ne sakataren cocin.

Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa Aminiya cewa, dattijon da ke matsayin jami’in koci na cocin ne ya kai kuɗin fansar, inda ’yan bindigar suka ƙi sakinsa bayan sun karɓi kuɗin.

Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto ’Yan bindiga sun harbe mata 2 a gona a Kogi

“An saki faston, amma suka ci gaba da tsare mutumin da ya kai musu kuɗin. Ba mu san dalili ba, muna cikin fargaba da alhini,” in ji majiyar.

An sace Fasto Ali, mai shekara 30, daga gidansa da misalin ƙarfe 1 na dare a ranar 8 ga Afrilu, ƙasa da makonni biyu da naɗa shi zuwa cocin.

Tun da farko, masu garkuwar sun buƙaci kuɗin fansa Naira miliyan ɗari (N100m) ne daga shugabannin cocin.

Ƙoƙarin Aminiya na jin ta bakin hukumomin tsaro bai ci nasara ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ECWA Karamar Hukumar Sanga

এছাড়াও পড়ুন:

Mai damfarar fursunoni ya gurfana a kotu a Kano

An gurfanar da wani mutum a gaban Kotun Majistare ta 17 a Kano bisa zargin shi da karɓar kuɗi a hannun wasu fursunoni da alƙawarin cewa zai fitar da su daga gidan yari.

Ana zargin wanda ake tuhumar, Kabiru Ahmed, da karɓar jimillar kuɗi naira dubu dari shida da goma daga Abdul Mukhtar, Bilkisu Shehu da kuma Muhammad Yahaya da sunan zai yi musu aiki a sako su daga gidan yari.

Lauyar masu gabatar da ƙara, Barista Sadiya Sabo, ta tuhumi mutumin da laifin damfara da kuma cin amanar da aka ba shi.

Wanda ake tuhuma ya amsa laifin, amma ya bayyana cewa ba shi kaɗai ya aikata wannan haramtaccen aiki ba.

’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya

Mai shari’a, Mai shari’a Hudu Haruna, ya bayar da umarnin mika wanda ake zargin ga ’yan sanda domin ci gaba da bincike, kuma ya ɗage shari’ar zuwa 20 ga watan Afrilu da muke ciki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • MDD Ta Bukaci Taimako Dangane Rikicin Sudan Wanda Ya Isa Kasar Chadi
  • Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing
  • ’Yan bindiga sun harbi alkali da ɗansa, sun sace mutane 13 a Katsina
  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 17: Tinubu Ya Kare Yadda Gwamnatinsa Ke Tafiyar Da Tsarin Rabon Arzikin Kasa
  • Mai damfarar fursunoni ya gurfana a kotu a Kano
  • Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet
  • An Sace Dalibin Jami’ar Tarayya Birnin Kebbi
  • Mata Sun Yi Zanga-zanga Kan Yawaitar Satar Mutane A Kogi