Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
Published: 12th, April 2025 GMT
Haka zalika, Kangye ya kuma tabbatar wa da al’umma cewa; jami’an tsaro na ci gaba da mayar da hankali wajen cafke fitaccen shugaban ‘yan ta’addan nan, Bello Turji.
Sannan, ya yi watsi da ikrarin da sojoji suka yi na cewa; sun dakile hare-haren makiyaya da ‘yan ta’adda da kuma barayin shanu da sauran makamantansu.
Da yake yin jawabi game da kyautata wa sojojin da suka jikkata, Kangye ya musanta zargin yin watsi da sojojin da suka samu raunuka.
Ya ce, “To, a iya sanina dangane da abin da hukumar sojoji ke yi, sojojinmu na samun isasshiyar kulawa, kuma kai dan jarida ne, da ka lura da lokacin hutun Sallah, za ka ga yadda babban hafsan soji da hafsan hafsoshin sojin sama da wasu manyan hafsoshi daga hedikwatar hukumar suka ziyarci sojojin, domin taya su murnar Sallah.
“Sannan kuma, zan iya fada muku cewa; hedikwatar rundunar sojojin Nijeriya, na kula da marasa lafiya da wadanda suka samu raunuka da wasu da ke bukatar a fitar da su zuwa kasashen waje, ana fitar da su, domin nema musu lafiya; wasu sun tafi Masar, wasu Turkiyya, wasu kuma Kasar Indiya. Kamar yadda muke magana yanzu, wasu har yanzu suna can suna samun kulawar likitoci a can.”
Ya kuma bayyana cewa, a ‘yan watannin da suka gabata, an raba wa sojojin da suka samu jikkata a fagen-daga gidaje.
Kangye ya kuma yi nuni da cewa, an raba wa sojojin da suka jikkatan gidajen kyauta ne, domin kuwa wasu daga cikinsu; ba za su iya dawowa fagen aiki ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nijar
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar Sojan Nijeriya Ta Fara Gasar Wasanni A Sakkwato
Runduna ta 8 ta sojojin Najeriya ta fara gasar wasanni ta kasa da ake gudanarwa duk shekara a jihar Sokoto da nufin karfafa sojojin Najeriya don shiryawa tsaron kasa.
Babban Jami’in Kwamandan runduna ta takwas Manjo Janar Ibikunle Ajose ya ce gasar tana nuni ne kai tsaye ga hafsan hafsoshin sojin kasar na ganin an gyara da sauya dabarun jagoranci da fagen fama a matakin farko.
GOC wanda ya samu wakilcin kwamandan runduna ta 78 da ke samar da kayayyaki da sufuri, Birgediya Janar Moses Udom Ikobah, ya bayyana cewa fafatawar ta yi daidai da kokarin da rundunar sojojin Najeriya ke yi na inganta yaki da ta’addanci ta fuskar tsaro.
Ya bukaci dukkan mahalarta taron da su kiyaye mafi girman matsayin wasanni, aiki tare, da rikon amana.
A jawabin maraba da Kwamandan, Birgediya Janar AbdulMalik Jibia Mohammed, shiyya ta 8, ya bayyana farin cikinsa da gudanar da taron tare da bayyana muhimmancinsa fiye da yadda ake gudanar da gasar.
Ya ce an shirya gasar ne domin karfafa kananan shugabanni, da karfafa kimar aikin soja, da kuma samar da kwakkwaran runduna a tsakanin sojoji da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin sassan, tare da kara kaimi, da juriya, da dabara na jami’an da ba manyan jami’ai ba.
Birgediya Janar Abdulmslik Jibia wanda ya ba da misali da dabarun da atisayen ke da su, ya ce gasar za ta kunshi abubuwa da dama da suka hada da karatun taswira, ninkaya, atisayen iri iri, da juriya, da sarrafa makamai, da nufin gwada shirye-shiryen yakar duk wani abin da zai taso.
Gidan Rediyon Najeriya dake Sokoto ya ruwaito cewa, taron wanda ya dauki tsawon mako guda ana gudanar da shi, ya tattaro tsare-tsare daga sassan sassan, da suka hada da bataliya ta 1 da 17 da 48 da 58, da kuma rundunar da aka kafa, duk sun fafata ba don daukaka ba, sai dai don nuna shirye-shiryensu na gudanar da aiki da kuma kwazonsu na kwarewa.
NASIR MALALI