Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza
Published: 12th, April 2025 GMT
Sojojin kasar Yemen sun yi amfani da jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa kan cibiyoyin makamai na HKI wadanda suka Yaffa (tel aviv) saboda daukar fansa kan kashe-kashen da take yi a Gaza.
Tashar talabijin Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran YAF na kasar Yemen yana fadar haka a jiya Jumma’a, ya kara da cewa sojojin yahudawan sun kai hare-hare kan unguwar Shaja’iyya inda suka kashe Falasdinawa da dama.
Ya zuwa yanzu tun fara yakin tufanul Aksa, a cikin watan Octoban shekara ta 2023, falasdinawa kimani 51,000 sannan wasu 115,688 a gaza. Ta kuma rusa kimani kasha 90% na gine-ginen Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
Isra’ila ta ce ta karbe iko da wata muhimmiyar hanya a zirin Gaza a wani mataki da ya yanke gaba daya yankin kudancin Rafah mai yawan jama’a daga sauran yankunan Falasdinawa da aka yiwa kawanya.
A cikin wata sanarwa da Isra’ila ta fitar yau Asabar ta ce dakarunta sun yi wa Rafah kawanya gaba daya tare da samar da “yankin tsaro” a can.
Sanarwar da ministan harkokin soji na gwamnatin Isra’ila Katz ya fitar ta ce sojojin sun karbe ikon “Morag axis, wanda ke ratsa Gaza tsakanin Rafah da Khan Yunis.”
Katz ya kuma yi kira ga Falasdinawa da su fara kaura zuwa yamma, yana mai gargadin cewa nan ba da jimawa ba za a kara kaimi da fadada ayyukan soji zuwa wasu yankuna a cikin mafi yawancin Gaza.
IDF ta ce ta karɓe da abin da ta bayyana da cibiyar tsaronta da ta yi wa laƙabi da ”Lungun Morag”, sunan wani ginin da Isra’ila ta taɓa yi tsakanin biranen biyu.
A yanzu haka sojojin Isra’ila na gina titi a wurin, da nufin samar da wani wuri da Isra’ila ke iko da shi da ya raba Zirin Gaza.
Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da Hamas ke cewa ta aika wakilanta zuwa Masar domin tattaunawa da masu shiga tsakani kan yiwuwar dawo da yarjejeniyar zaman lafiya.