Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-12@21:43:50 GMT

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Published: 12th, April 2025 GMT

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta samar da ababen hawa ga shugabannin makarantun babbar  sakandare a fadin jihar.

Kwamishinan ilimi na jihar, Farfesa Isa Yusuf Chamo, ne ya bayyana hakan yayin wani taro da ya gudanar da shugabannin makarantu a garin Dutse.

A cewarsa, za a gyara gidajen ma’aikatan makarantun sakandare domin saukaka matsalar masauki ga malamai da sauran ma’aikata da ba malamai ba.

Farfesa Chamo, wanda Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Harkokin Ilimi, Malam Abdullahi Hudu, ya wakilta, ya ce taron ya na da nufin tattauna shirin dawowa  makarantu bayan hutun da aka yi a jihar.

Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta sanya bangaren ilimi a sahun gaba saboda muhimmancinsa ga ci gaban jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa gwamnatin jihar ta dauki malamai 7,000 domin inganta tsarin koyarwa a makarantu, inda ya kara da cewa za a dauki ma’aikatan girki na J-Cook domin kara karfafa harkar gudanarwar makarantu.

A jawabansu daban-daban, wasu daga cikin Daraktoci da Shugabannin makarantu, sun bukaci a sake duba kudaden gudanar da makarantu, da samar da kwamfutoci da kayan aikinsu, da bayar da tallafi da kuma samar da malamai domin inganta ayyukan koyarwa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Na Jihar Jigawa Ya Cancanci Karramawar LEADERSHIP – Hamisu Gumel

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
  • Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (1)
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
  • Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji
  • Gwamna Namadi Na Jihar Jigawa Ya Cancanci Karramawar LEADERSHIP – Hamisu Gumel
  • Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar
  • UBEC Ta Yaba Wa Jigawa Kan Inganta Harkar Ilimi A Jihar
  • Femi Falana SAN Ya Yi Kiran A Inganta Harkar Shari’a A Najeriya
  • Malaman Makarantun Firamare 1,800 Sun Samu Horo Aka A Kwara