Za a ci gaba da tunawa da shi a matsayin ɗaya daga cikin fitattun ‘yan wasan Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Rasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 108

108-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na Kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin al-kur’ani  mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da Littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawi na maulana Jalaluddin Rumi, ko kuma cikin wasu littafan. Da fatana masu sauraro zasu kasance tare da mu.

///.. Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan lamami na biyu daga limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All…(s) kuma da na farko ga Fatimah (s) diyar manzon All..(s).

A cikin shirimmu da ya gabata mun kawo maku yadda Khalifa Uthman ya tura walidu dan Ukuba dan Abu muid a matsayin walin Kufa, mun kuma ji irin barnan da yayi, da baitul malin musulmi, ya sha giya ya bada sallar Asubaha, raka’o’ii 4 sannan ya juya yace in kara maku ne.

Banda haka, yana yayi aman giyar a cikin masallaci, sannan yana sanya zoben zinari wanda aka haramtawa mazaje sanya shi. Har’ila yau munji yadda Khalifa Uthman bai ji dadin wadanda suka kawo kararsa daga kufa ba, sai da suka sami mafaka wajen Amirul muminina,(a) wanda ya yiwa Khalifa magana a kansa, sannan ya amince ya tube shi ya kuma dawo da shi Madina, aka tabbatar da shaidar cewa ya sha giya, amma an kasa samun wanda zai yi masa haddi, saboda kusancinsa da Khalifa, sai Imam Ali (a).  Wanda ya tashi ya dauko bulala ya kuma tsaida haddin All..a kansa.

Sannan mun yi yadda manzon All..(s) ya bada umurnin a kashe baban Walid bayan an kamashi cikin fursinonin da aka kama a Badar, saboda tufa yawun da ya yi a furkar manzon All..(s) a Makka, sannan ya zage shi. Sannan mun ji cewa All..ya sauko da yar Alkur’ani mai girma yana kiran walid dan Ukba a matsayin fasiki, saboda kariyar da yayiwa manzon All..(s) dangane da da Banu Mustalak.

Don haka mukace saboda wannan da kuma wasu abubuwa bai kamata a ce irin wannan mutum ya zama shugaban al-ummar musulmi musamman manya-manyan garuruwan da suke da baki sabbin musulunta wadanda suke bukatar ilmin addinin da halaye masu kyau a wajen shuwagabannin musulmi don su koyi addinin musulunci su kuma iya rikeshi ba. Koma wadanda basu musulunta daga cikinsu su musulunta ba.

Daga nan sai Khalifa ya nada Sa’id dan Ass a matsayin gwamnan Kufa, shima daga cikin dangin Uthman, kuma shi yaro ne matashi wanda, yake cikin bai da kamun kai, don haka ne ma, mutanen Kufa, bayan sun je cewa Khalifa ya aiko Sa’ida dan Ass a matsayin walin kufa sun taru sun hana shi shiga garin. Sai dai daga bayan an fi karfinsu, inda khalifa ya bada umurni a koresu daga Kufa zuwa sham, wajen Mu’awiya dan Abi Sufyan, sun je mu’awiya ya basu masaiki mai kyau kuma yana kola da su tare da kokarin janra’ayinsa su mika kai ga banu Umayya, amma bayan wani lokaci ya ga cewa ba wani ci gaba, kuma zamansu a sham ma zai iya zama hatsari gareshi. Sai ya rubuta Khalifa Uthman kan cewa ba zai iya ci gaba da ajiyesu a sham ba.

Khalifa ya sake maida su Kufa wajen Sa’id dan Ass, sai wata rana sa’ida ya tare mutane a kasar Azumi ya ce masu wa yaga wata sai wani sahabi mai suna Hashin dan Utmah, ya ce ya gaba wata, sai sa’id ya ce masa da wannan idonka da baya gani ne ka ga watan ?.

Sai Hashim, ya ce, masa kana aibatani da wannan idan, an ji mani ciwo ne a idon kan tafarkin All.. a yakin Yarmuk ne ya rasa idonsa guda. Don haka Hashim ya ta shi da safe ba tare da azumi ba, yayi sallah, sai mutane da dama suka sha ruwa saboda ya ce ya gani, don shi ba makaho ne kwata-kwata ba. Kuma manzon All..(s) ya ce ” Ku yi azumi da gani ku kuma ajiye azumi da ganin jinjirin wata.

A lokacinda Sa’id ya ji cewa Sa’id yayi salla kuma mutane da dama sun bishi, sai ya sa aka kama shi aka kawo shi gidan sa,  ya sa aka dakeshi aka kuma kona gidansa.  A cikin wannan halin sai Malik dan Ashtar daya daga cikin shuwagabannin kabilun yemen a Kofa ya ji sa’ida yana cewa: A dukiyar kufa gaba daya mallakin shi da kuma banu Umayya ne.

Sai ta tashi yayi masa inkari, sannan malamai da mahaddatan alkur’ani a Kufa sun goyi bayansa. A lokacinda dogarin sa’id ya ga haka, sai yah au kansu, suka taru suka yi masa duka har ya suma.

A nan sai Sa’id ya rubuta wasika zuwa ga Khalifa Uthman wanda ya bada umurnin a koresu daga Kufa zuwa Sham, wanda muka yi magananrsa a baya.

Bayan da mu’awiya yak asa zama da su ne sai Khalifa ya ce Sa’id ya koresu zuwa Khum na kasar ta sham amma karkashin Abdurrahman dan Khalid bin Walid sai suka koma Khums , Abdurrahman ya wahalar da su so sai.

Sai suka fadawa Abdurrahman ya nemammasu Afwa daga Uthman a lokacinda ya yi masu fawa suka koma kufa sai suka sake fitowa zuwa Madina inda suka bukaci Uthman ya tube masu sa’id ya ki yin haka, sai Sa’idu ya Je madina don wata bukatarsa, zai sake komawa Kufa sai Malik da sauransu suka ce ba zai sake komawa Kofa ba, suka zare takubbansu, sai dai a yi yaki. Don haka ala tilas Uthman ya tube shi ya aiko masu da wani.

Haka ma a Basra, Uthman ya tube Abu Musa Al-ashari ya maye gurbinsa da wani matashi dan kawwar mahaifiyarsa, Abdullahi dan Amiru wanda baifi shekaru 25 a duniya ba.

Mutanen Basra sun yi ta korafi amma ya ki ya cire shi. Ya ci gaba da kasancewa walin Basra har zuwa lokacinda ya ji labarin an kashe Uthman ya yawushen baitul  Mali ya arce zuwa Makka, inda ya hadu da A’isha da Talha da Zubair, har zuwa lokacinda suka Imam Ali (s) ya yake su a Basra ya kuma sami galaba a kansu.

04-Mu’awiya dan Abisufyan, wanda ya kasance dan Abu sufyan, kuma gwamna a kasar sham tun lokacin Khalifa na biyu. A cikin sirar Khalifa Umar yakan sanya gwamnoni ko wali a yankunar daular musulunci ya kuma tubesu tare da karamin laifi ko kuma babu wani laifin da suka yi, sai idan ya ga dama sai ya saukesu kawai.

Amma tunda ya dora mu’awiya kan kasar sham bai tabe shi ba, banda haka yana kara masa karfi.

Tun lokacinda ya dorashi kan aiki a kasar sham da urdon bai sauke shi ba. Sannan idan wani ya kawo masa sukansa, na cewa yana al-mubazzaranci, yana sanya rigunan da suka haramta a musulunci, sai Khalifa Umar yace: Ai wannan hi ne kisran musulmi.

Khalifa Umar yakan yi hisabiwa gwamnoninsa a ko wace shekara, sannan yakan raba dukiyoyin biyu ya dauki rabi ya maida shi madina, wannan dukiyoyin da suka samu ta hanyar Halar wato ta kasuwanci ko kuma, wasu hanyoyin da suka dace.

Amma banda  mu’awiya dan Abusufyan, shi yana kashe kudade jama’a yana rayuwa irin ta sarakuna, amma sai ya rufe idanunsa  kamar bai gani ba. Wannan halin haka ya tafi har ya bar duniya.

Sannan a lokacinda zai rasu, khalifa Umar ya fadawa wadannan mutane 6 wadanda yace manzon All..(s) ya rasu yana mai yarda da su kan cewa, idan sun ta hasada a tsakaninsu, sun rigima a tsakaninsu, to mu’awiya zai yi maganinsu.

Wannan ya nuna cewa sun shirya Mu’awiya a kasar Sham ne don ya zama Khalifa, a wani lokaci nan gaba. Ko kuma ya kwace khalifanci, daga khalifa a Madina, ya maida ita cikin bani Umayya wadanda suka yaki manzon All…(s) har zuwa Fatahin Makka. Kuma abinda ya faru kenen bayan shahadar Amirul Mumimnina (a).

Don mu’awiya ya yi karsfi a kasashen shammat guda 4, siriya lebanin Urdun da Falasdin, sannan a likacin Uthman ya karawa mu’awiya wasu yankuna kamar Khums. Don haka sojojinsa sun fi karfin sojojin da zasu fito daga Madina in da za’a yi yaki ne a tsakaninsu. Sannan ga duniya ga kuma biyya wanda mutanen sham suke masa. Basa saba masa, suna sonsa yana sonsu, basu san wani musulunci bas ai wanda Mu’awiya dan abi Sufyan ya fada masu. Daga cikin ya fada masu cewa Aliyu dan Abitalib (a) bayan sallah. A lokacinda suka ji labari an kashe shi a masallaci yana bada sallah, sai suka ce, shin yana sallah ne?.

Don haka bayan kissan khalifa na biyu, Sai aka zabi Uthman a matsayin Khalifa a bayansa, ya tabbatar da mu’awiya a matsayinsa tunda shi dangin Banu Umayya ne, don haka, na gida ne ya sami iko, ya zama khalifa. Don haka bamu taba jin wani sabani tsakanin mu’awiya da khalifa Uthman ba, har aka kashe shi bayan shekaru kimani 12 da Khalifanci. Banda haka a lokacin Khalifancinsa yak ara karfafa shi kamar yadda muka fada.  

Don haka zamu iya cewa ba wanda ya sami rabo mai tsoka daga cikin dangin Banu umayya daga wajen Khalifa Uthman kamar yadda Mu’awiya ya samu. Don a lokacinda yake mulkin kasar sham kamar sarki ne mai zaman kansa. Daga lokacin Khalifa Umar har zuwa kissan Khalifa Uthman, mu’awiya ya yi kimani shekaru 20 yana sarauta a Sham.

Don haka ba sai mun yawaita magana a kansa a yanzu, ba, sai nan gaba, a lokacinda Imam Ali ya zama Khalifa sannan mu’awiya yace ba zai yi masa bai’a ba. Da kuma abubuwa da suka biyu baya, har ya kwace iko da Imam Hassan (a).

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shrimmu na yau sai kuma wata Fitowa idan All..ya kaimu wassalamu a laikum wa rahamatullahi wa barakatuhu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • Abubuwa Da Yawa Na Faruwa Ba Tare Da Sanin Tinubu Ba – Tsohon Ma’aikacin Aso Rock
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 108
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
  • Har Yanzu Shugabanci NNPP Na Hannunmu – Tsagin Kwankwaso
  • Salah Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniyar Shekaru 2 Da Liverpool
  • Huawei Ya Daddale Yarjejeniya Da Kenya Don Habaka Kwarewar Ma’aikatan Kasar A Fannin Dijital
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur 
  • Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Zakarun Turai A Karon Farko Bayan Shekaru 10