Aminiya:
2025-04-13@09:21:24 GMT

Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu

Published: 13th, April 2025 GMT

Tsohon ɗan wasa, kuma tsohon mai horas da ’yan ƙwallon Super Eagles ta Najeriya, Christian Chukwu ya rasu.

Christian Chukwu ya rasu ranar Asabar yana da shekara 74.

Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato

Christian Chukwu ne kyaftin ɗin tawagar Super Eagles lokacin da Najeriya ta lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka (AFCON) ta 1980.

Dakta Olusegun Odegbami, tsohon ɗan wasan Najeriya kuma abokin Chukwu, ya tabbatar rasuwar mai ban tausayi a saƙon da ya wallafa ta manhajar sada zumunta X.

“Na samu labarin cewa tsakanin ƙarfe 9:00 zuwa 10:00 na safiyar yau Asabar, Christian Chukwu, MFR, wanda aka fi sani da Chairman abokina kuma abokin wasana, ɗaya daga cikin manyan ’yan wasan ƙwallon ƙafa a tarihin Najeriya, ya rasu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Super Eagles ta Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar Sojan Nijeriya Ta Fara Gasar Wasanni A Sakkwato

Runduna ta 8 ta sojojin Najeriya ta fara gasar wasanni ta kasa da ake gudanarwa duk shekara a jihar Sokoto da nufin karfafa sojojin Najeriya don shiryawa tsaron kasa.

 

Babban Jami’in Kwamandan runduna ta takwas Manjo Janar Ibikunle Ajose ya ce gasar tana nuni ne kai tsaye ga hafsan hafsoshin sojin kasar na ganin an gyara da sauya dabarun jagoranci da fagen fama a matakin farko.

 

GOC wanda ya samu wakilcin kwamandan runduna ta 78 da ke samar da kayayyaki da sufuri, Birgediya Janar Moses Udom Ikobah, ya bayyana cewa fafatawar ta yi daidai da kokarin da rundunar sojojin Najeriya ke yi na inganta yaki da ta’addanci ta fuskar tsaro.

 

Ya bukaci dukkan mahalarta taron da su kiyaye mafi girman matsayin wasanni, aiki tare, da rikon amana.

 

A jawabin maraba da Kwamandan, Birgediya Janar AbdulMalik Jibia Mohammed, shiyya ta 8, ya bayyana farin cikinsa da gudanar da taron tare da bayyana muhimmancinsa fiye da yadda ake gudanar da gasar.

 

Ya ce an shirya gasar ne domin karfafa kananan shugabanni, da karfafa kimar aikin soja, da kuma samar da kwakkwaran runduna a tsakanin sojoji da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin sassan, tare da kara kaimi, da juriya, da dabara na jami’an da ba manyan jami’ai ba.

 

Birgediya Janar Abdulmslik Jibia wanda ya ba da misali da dabarun da atisayen ke da su, ya ce gasar za ta kunshi abubuwa da dama da suka hada da karatun taswira, ninkaya, atisayen iri iri, da juriya, da sarrafa makamai, da nufin gwada shirye-shiryen yakar duk wani abin da zai taso.

 

Gidan Rediyon Najeriya dake Sokoto ya ruwaito cewa, taron wanda ya dauki tsawon mako guda ana gudanar da shi, ya tattaro tsare-tsare daga sassan sassan, da suka hada da bataliya ta 1 da 17 da 48 da 58, da kuma rundunar da aka kafa, duk sun fafata ba don daukaka ba, sai dai don nuna shirye-shiryensu na gudanar da aiki da kuma kwazonsu na kwarewa.

 

NASIR MALALI

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon Kocin Super Eagles, Christian Chukwu, Ya Rasu Yana Da Shekaru 74
  • Abubuwa Da Yawa Na Faruwa Ba Tare Da Sanin Tinubu Ba – Tsohon Ma’aikacin Aso Rock
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya
  • Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet
  • NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma
  • Rundunar Sojan Nijeriya Ta Fara Gasar Wasanni A Sakkwato
  • Femi Falana SAN Ya Yi Kiran A Inganta Harkar Shari’a A Najeriya