Wata kotu a Amurka ta umurci Hukumar Binciken Manyan Laifuka ta ƙasar (FBI) da ta fitar da bayanan sirri da aka samu kan Shugaba Bola Tinubu a lokacin wani binciken badaƙalar miyagun ƙwayoyi da gwamnatin ƙasar ta yi a shekarun 1990.

Jaridar Premium Times ta ruwaito Alƙalin kotun, Beryl Howell wanda ya ba da umarnin a ranar Talata, yana mai cewa babu ma’ana a rufe bayanan ba tare da an bayyana wa jama’a ba.

’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasar

A watan Yunin 2023 ce wani Ba’Amurke, Aaron Greenspan, a ƙarƙashin dokar ’yancin fitar da bayanai (FOAI) ya miƙa buƙatar a ofishin zartarwa na lauyoyin Amurka, da Hukumar FBI da Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (DEA) da kuma Hukumar Leƙen Asiri ta (CIA).

Wasu bayanai na cewa, a shekarar 1993 ce Tinubu ya sarayar da kimanin Dala 460,000 ga gwamnatin Amurka bayan mahukunta sun alaƙanta kuɗin da fataucin miyagun ƙwayoyi.

Ana iya tun cewa, wannan hujja ta rashin cancantar tsayawa takara manyan ’yan adawar Shugaba Tinubu — Atiku Abubakar da Peter Obi — suka gabatar a yayin ƙorafin zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

Sai dai kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen ta yi watsi da ita tana mai tabbatar da nasarar Tinubu a babban zaɓen ƙasar ma 2023.

 

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan

Hukumar kula da agaji ta MDD (OCHA) ta bada sanarwan cewa, gwamnatin HKI a yankin yamma da kogin Jordan ta kori Falasdinawa a gidaje 5 a yankin bayan sun rusa gidajensu. Hukumar ta kara da cewa wadanda HKI ta rusa gidajensu a yankin sun hada da yara 19 da da iyayensu 33 maza da mata 6.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto OCHA na cewa tun watan Maris da ya gabata zuwa yanzu, HKI ta rusa gidaje da gine-ginen Fafalsadinawa kimani 100 a yankin yamma da kogin Jordan wadanda suka hada da gabacin birnin Qudus da kuma sauran yankuna, da sunan an gina gidajen ba bisa ka’ida ba.

Banda haka suna kwace gonakin Falasdinawa don ginawa sabin yahudawan da suke shigowa kasar matsugunai.

Labarin y ace, a wasu lokutan yahudawan zasu tilastawa Falasdinawa rusa gidajensu da kansu ko kuma idan sun rusa su da kayan aikinsu su tilastawa Falasdinawan kbiyan kudaden aikin rusawan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
  • Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
  • An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Vietnam
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • An kama miyagun kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasar
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu