NATE Ta Rantsarda Sabbin Shugabanni Reshen Jihar Kaduna
Published: 13th, April 2025 GMT
Kungiyar Kwararrun Masu Fasahar Injiniya ta Ƙasa (NATE) ta rantsar da sabbin shugabannin reshen Jihar Kaduna da za su jagoranci harkokin kungiyar a jihar.
Mataimakin Shugaban Yankin Arewa maso Yamma na NATE, Injiniya Bala Muhammad, yayin bikin rantsarwa da aka gudanar a Kaduna, ya bukaci sabbin shugabannin da su fifita haɗin kai da ci gaban ƙungiyar.
Sabbin shugabannin da aka rantsar sun hada da: Injiniya Audu John a matsayin Shugaba, AbdulKadir Julde a matsayin Mataimakin Shugaba, sannan Williams Okonkwu a matsayin Sakataren reshen.
Sauran su ne Sim Marca Maikege a matsayin Ma’ajin Kuɗi, AbdulGaniu Isah a matsayin Sakataren Kuɗi, da Racheal Ovbiagele a matsayin Sakataren Fasaha.
Haka kuma, Engr. Ishaya Buba daga Radio Nigeria Kaduna ya zama Jami’in Hulɗa da Jama’a, Khadijah Abdullahi a matsayin Ko’odinetan Mata, sannan Aliyu Ibrahim Usman a matsayin Sakataren Membobinsu.
Matsayin Mai Bincike (Auditor) da Mataimakin Sakatari suna nan a buɗe, ba a cike su ba tukuna.
A jawabinsa na kama aiki, sabon Shugaban, Injiniya Audu John, ya jaddada muhimmancin jajircewar mambobi, musamman ta fuskar biyan kuɗin zama dan kungiya da kuma kuden cigaba da zama dan kungiya wato (check-off dues).
Ya ce babu wata ƙungiya da za ta samu ci gaba idan ba tare da sadaukarwar mambobinta ba, kuma za su baiwa wannan bangare muhimmanci sosai.
Injiniya Audu John ya kuma bayyana shirin hadin gwiwa da manyan abokan hulɗa, musamman a sashen masana’antu, gwamnati da masu zaman kansu, domin tabbatar da cewa mambobin kungiyar sun samu wakilci da tallafi yadda ya kamata.
A cewarsa, shugabannin da suka gabata sun fara irin wannan aiki ta hanyar kai ziyarar girmamawa zuwa kamfanonin Nocaco Nigeria Limited da Hukumar Albarkatun Ruwa domin tantance mambobi da kuma farfado da hulɗar hadin gwiwa.
Shugaba Audu ya yaba wa Kwamitin Zaɓe karkashin jagorancin Engr. Silas Oluyori bisa gudanar da zaɓe mai tsafta, adalci da gaskiya duk da kalubalen da suka fuskanta.
A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Yanki Arewa maso Yamma, Injiniya Bala Muhammad, wanda Jami’in ƙasa na NATE, Injiniya Lukman Sani ya wakilta, ya bayyana cewa reshen Kaduna ne tushen dukkanin rassan NATE a yankin Arewa maso Yamma, amma har yanzu yana fama da kalubale.
Ya bukaci sabbin shugabannin su yi aiki tare da juna don dawo da karfin da kuzarin reshen Kaduna kamar yadda aka san shi a da.
Ya taya kwamitin zaɓe murna bisa gudanar da zaɓen cikin nasara, tare da tabbatar da ci gaba da tallafa musu don cigaban reshen jihar.
Tun da farko a jawabin sa, Shugaban Kwamitin Zaɓe, Engr. Silas Oluyori, ya gode wa duk masu ruwa da tsaki a kungiyar bisa goyon bayan da suka bayar, wanda ya taimaka sosai wajen shawo kan matsalolin da suka fuskanta a lokacin shirya zaɓen.
A zantawa da manema labarai, sabon Jami’in Hulɗa da Jama’a, Engr. Ishaya Buba, na gidan Radio Nigeria Kaduna ya bayyana cewa sabbin shugabannin za su kawo sauyi mai amfani wanda zai ɗaga darajar ƙungiyar zuwa mataki mafi girma.
Ya ce, cancanta da jajircewar sabbin shugabannin na nuna alamar cewa za su taka rawa ta kwarai wajen jagoranci da kawo ci gaba mai ma’ana ga reshen Kaduna.
REL: Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamnati Kaduna Jihar Rantsarda
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce shirye-shirye sun yi nisa game da aikin Hajjin shekarar 2025 a jihar.
Daraktan Hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga Radio Nigeria a hedikwatar hukumar da ke Dutse.
A cewarsa, zuwa yanzu hukumar ta mika sunayen maniyyata fiye da dubu ɗaya da suka kammala biyan kuɗin aikin Hajji daga jihar zuwa ga Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON).
Ya ce tuni aka fara shigar da waɗanda suka kammala biyan kuɗin cikin tsarin neman biza.
Labbo ya bayyana cewa hukumar ta biya Hukumar Hajji ta Ƙasa kuɗi naira biliyan takwas a madadin alhazan jihar na shekarar 2025.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce ana gudanar da tarukan bita ga maniyyata a kullum, a kananan hukumomi 27 na jihar, ta hannun wasu malamai don ilmantar da su game da aikin hajjin.
Ya ƙara da cewa hukumar za ta raba jakunkuna da za su daukin nauyin kilo 8 da unifom ga jami’an yankuna da cibiyoyi domin rabawa mahajjatan.
Shugaban hukumar ya ja hankalin maniyyatan da su riƙa halartar traon bita saboda muhimmancinsa.
Ya yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da haɗin kai da yake ba hukumar domin samun nasarar gudanar da aikin hajji ba tare da wata tangarda ba.
Radio Nigeria ta ruwaito cewa Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta ware kujeru sama da 1,800 ga jihar domin aikin hajjin bana.
Usman Muhammad Zaria