Aminiya:
2025-04-15@19:58:00 GMT

Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato

Published: 14th, April 2025 GMT

Kasurgumin dan ta’addar nan da ke addabar yankin Sakkwato ta Gabas da Zamfara, Kacalla Bello Turji ya kashe manoma 11 a garin Lugu cikin Karamar Hukumar Isa ta Jihar Sakkwato.

Dan gwagwarmaya da ke biye da lamarin rashin tsaro a yankin Sakkwato ta Gabas Bashiru Altine Guyawa ya sanar wa manema labarai cewa, Turji ya dawo daga yawon sallah ne ya far wa garin da hari.

’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume

“Turji da yaransa sun bar kauyensa na Fakai a Karamar Hukumar Shinkafi suka shiga wasu kauyukka a Karamar Hukumar Isa a hanyarsu ta komawa Fakai bayan sun gama yawon Sallah suka kashe manoma 11.”

Guyawa yana ganin laifin jami’an tsaro kan lamari, inda suka gaza daukar mataki kan bayanan sirri da suke da shi.

Dan majalisar dokokin jiha, Honarabul Aminu Boza ya ce, ya samu bayanin sai dai dan bindigar bai shiga yankin da yake wakilta ba a lokacin bikin Sallah.

Ya ce, “muna sane da cewa Turji ya shirya kai ziyara a gabashin Gatawa, a nan ne muka dauki mataki, mun je Sabon Birni, inda muka dauki matakin tsaro don kare faruwar hakan, shi ne dalilin huce haushinsa a kan manoma a Isa’’.

Akwai bayanan da ke nuna cewa, Turji ya tsaya a kauyen Tozai, ya kashe shugaban ‘yan sintiri na garin.

A lokacin da aka tuntubi Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yan sandan Jihar Sakkwato, ASP Ahmad Rufa’i ya ce, jami’an soja ne kadai za su iya tabbatar da farmakin saboda su ne ke aiki a yankin.

Duk da sojoji sun ayyana suna neman Turji ruwa jallo, amma ya ci gaba da kai farmaki a kauyukkan gabashin Sakkwato.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato Jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba

Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya  zai ziyarci Tehran a ranar Laraba mai zuwa.

Ziyarar ta Grossi na zuwa ne gabanin sabuwar tattaunawar da za’ayi tsakanin Iran da Amurka a ranar Asabar mai zuwa kan batun shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin kasa da kasa Kazem Gharibabadi ya ce shugaban hukumar ta IAEA Rafael Grossi zai ziyarci Tehran a ranar Laraba.  

Gharibabadi ya bayyana cewa, babban daraktan hukumar ta IAEA, zai gana da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) Mohammad Eslami.

Ya kara da cewa “ziyarar na cikin tsarin ci gaba da hulda da hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu.”

Ziyarar ta shugaban hukumar ta IAEA za ta zo ne a daidai lokacin da Iran da Amurka ke shirin gudanar da tattaunawar ta biyu, wanda Oman ta shiga tsakani a ranar Asabar data gabata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
  • An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya
  • Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • An Karrama Shugaban Qausain TV, Kanar Sani Bello Da Lambar Yabo
  • An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • An kama miyagun kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano