Aminiya:
2025-04-19@19:18:07 GMT

’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta

Published: 14th, April 2025 GMT

Wata ’yar kasar Jamus mai suna Alexandra Hildebrandt mai shekara 66 ta ja hankalin jama’a bayan ta haifi ɗanta na 10 ba tare da maganin haihuwa ba.

Haihuwar ta faru ne a ranar 19 ga Maris a Asibitin Charité da ke Berlin da taimakon likita.

Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato

Ta bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da ta yi da Jaridar TODAY.

com a ranar Laraba, 26 ga watan Maris.

A cewar Hildebrandt, ta rawa wa jaririn suna Philipp, wanda ya zo da nauyin kilo 7, kuma yana cikin koshin lafiya.

Ta bayyana shi a matsayin wanda ya dace da ’ya’yanta da ke da yawa, wanda ya haɗa da yara masu shekaru tsakanin 2 zuwa 46.

“Babban iyali ba kawai wani abu ne mai ban mamaki ba, amma duk da haka, yana da mahimmanci don renon yara yadda ya kamata,” in ji ta a cikin imel.

Hildebrandt, wanda ke kula da gidan tarihi na Wall Museum a Checkpoint Charlie a Berlin, ba bakon abu ba ne wajen jan hankalin jama’a.

Rayuwarta cike take da tarihi, domin zama uwa a wurinta abin mamaki ne.

Duk da shekarunta, ta nace cewa ciki ba a tsara shi ta hanyar kimiyya, amma ya faru ne ta dabi’a.

Mahaifiyar ta bayyana cewa, tana rayuwa cikin matukar aiki.

Kafin haihuwar Philipp, ta bayyana wa Jaridar Jamus ta Bild cewa, “Ina cin abinci cikin koshin lafiya, ina iya yin ninkaya tsawon awa guda a matsayin motsa jiki kuma ina tafiyar tsawon awa biyu.”

Likitanta, Dokta Wolfgang Henrich ya tabbatar da cewa, cikin nata ya daidaita, yana mai bayyana shi a matsayin cikin da ba shi da matsala sosai,” kodayake Hildebrandt ta yi haihuwa takwas a baya duk ta hanyar tiyata.

‘Ya’ayanta 10 sun hada da tagwaye, Elisabeth da Madimilian, dukansu shekarunsu 12, wadanda suke nuna cewa, rayuwar Hildebrandt a matsayin uwa cike take da matakai iri-iri.

Amma haihuwar ’ya’ya a irin waɗannan shekarun na tsufa ba kowa ba ne ke samun hakan.

Henrich ya yi gargaɗin cewa, masu juna biyu a shekarun tsufa na rayuwa cikin haɗari.

Ya bayyana cewa, “matsaloli irin su hawan jini da haihuwar jariri kafin mako 37 da kuma al’amurran da suka shafi zuciya da jijiyoyin jini yawanci na karuwa da shekaru”.

Ta ce, tana ta samun sakonnin taya murna da soyayya daga abokanta da danginta bayan sanar da haihuwar Philipp.

“Na yi ta samun sakonnin fatan alheri,” in ji ta TODAY.com.

A halin da ake ciki, masana kiwon lafiya sun yi imanin cewa, ba koyaushe shekaru suke taƙaita batun haihuwa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haihuwa

এছাড়াও পড়ুন:

An tsinci gawar mabaraci mai shekara 75 a Neja

An tsinci gawar wani tsoho mai suna Haruna Abdullahi mai shekara 75 daga garin Gumel na Jihar Jigawa a ƙofar babbar kasuwar Kure Ultra Modern Market da ke Minna a Jihar Neja.

Babu wanda zai iya cewa ga musabbabin mutuwarsa, amma ’yan kasuwa sun shaida wa Daily Trust  cewa, an tsinci gawarsa da safiyar ranar Juma’a a babbar ƙofar shiga kasuwar.

Ya kashe masoyin tsohuwar matarsa bayan sakinta a Neja PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike

Kakakin rundunar ’Yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun ya tabbatar wa Daily Trust faruwar lamarin.

Ya ce, “A yau Juma’a 18/4/2025 da sanyin safiya, an tsinci gawar wani wanda aka bayyana sunansa da Haruna Abdullahi mai kimanin shekara 75 a ƙofar shiga kasuwar Kure.

“An ce mabaraci ne, kuma Bahaushe ne, ɗan jihar Gumel ne, kuma ba a ga wani alamar tashin hankali ba a jikinsa, an kai shi asibiti aka tabbatar da mutuwarsa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi
  • Manyan jami’an gwamnati sun halarci auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi
  • Babu wanda ya hana Shettima shiga Aso Rock ba— Fadar Shugaban Ƙasa
  • Makarantar Bare: Shekara 20 dalibai na karatu a matsanancin yanayi
  • An tsinci gawar mabaraci mai shekara 75 a Neja
  • BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano
  • Matar gwamna ta ɗauki nauyin ragon suna da hidimar duk matar da ta haifi ’yan uku a Sakkwato
  • ’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta
  • Batawa Sin Suna Ba Zai Taimaka Kawar Da Tambarin Amurka A Matsayin Daular Kutsen Intanet Ba