Aminiya:
2025-04-16@00:24:09 GMT

EFCC ta gaza tabbatar da tuhumar Murja kan zargin wulaƙanta takardar Naira

Published: 15th, April 2025 GMT

Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati, ta gaza tabbatar da zargin wulaƙanta takardar Naira da take yi wa fitacciyar ’yar TikTok ɗin nan, Murja Ibrahim Kunya.

A bayan nan ne EFCC ta gurfanar da Murja a gaban kotu kan zargin cewa ta ci karo da wani bidiyonta tana rawa a kan takardun kuɗi har kimanin Naira dubu 400.

A ƙunshin ƙarar da EFCC ta gabatar mai lamba FHC/KN/CS/18/2025 a gaban wata Kotun Tarayya da ke zamanta a Kano, ta ce laifin da take tuhumar Murja tanadi na Kundin Dokokin Babban Bankin Nijeriya CBN wanda ya haramta wulaƙanta takardar Naira ta kowace siga.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Murja Ibrahim Kunya Wulaƙanta Takardar Naira

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza

Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 tare da jikkata wasu 69 a cikin awa 24 a yankin Gaza, inda ta kai harin sama a wani asibiti da ke yankin Khan Younis.

Ma’aikatar Lafiyar Gaza ta sanar cewa jiragen Isra’ila sun kashe wani jami’in lafiya tare da jikkata wasu tara a Asibitin Kuwaiti da ke yankin Al-Musawi da ke Khan birnin Younis da ke Gabashin Gaza.

Mai magana da yawun asibitin, Saber Mohammed, ya bayyana cewa wadanda harin ya rutsa da su sun hada da marasa lafiya da kuma jami’an kiwon lafiya.

Isra’ila ba ta uffan a game da harin ba a halin yanzu, amma wasu rahotanni sun nuna jami’an tsaronta sun yi awon gaba da wasu Palasdinawa 14 a yankin Yamamcin Kogin Jordan.

Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato

Ofishin Kula da Fursunoni na Palasdinawa ya bayyana cewa yanacin mutanen an kama su ne a yankin Birnin Kudu, inda aka kama mutum uku a unguwar al-Issawiyya da ke Gabashin Birnin Kudus da wasu uku a garin Anata.

A yankin Ramallah kuma na jami’an Isra’ila sun kama Palasinawa uku a garin Al-Mazarra’a Ash-Sharqiya da kuma wani mutum guda a kauyen Kobar.

Sun kuma kama wani mutum guda a unguwar Ezbet al-Jarad da ke birin Tulkarem da wani guda kuma a Ezbet al-Tayah.A yankin Nablu kuma Isra’ila ta kama Palasdinawa uku a yankunan Beit Furik da kuma birnin Nablus.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Budurwar da ke rayuwa a banɗaki don gudun biyan kuɗin hayar gida
  • Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC
  • EFCC Ta Gurfanar Da Ɗan China A Kotu Kan Bayar Da Bayanan Ƙarya
  • Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
  • Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal