Lauyoyin Landan suna tattara bayanai kan ‘yan Birtaniya da suka yi aiki a cikin rundunar sojojin mamayar Isra’ila

Kwararru kan harkokin shari’a na kasar Biritaniya sun ce gurfanar da wasu ‘yan kasar masu takardar ‘yan kasa biyu da ke aiki a cikin sojojin mamayar Isra’ila a gaban kuliya bisa zargin hannu a tafka laifukan yaki a Gaza, zai yi tasiri ga wadanda ke tunanin shiga cikin sahunsu.

Hakan ya biyo bayan gabatar da rahoto ga rundunar ‘yan sandan birnin Landan ne mai kunshe da shaidun da suka shafi ‘yan Birtaniya guda 10 da suka yi aikin soja karkashin rundunar mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila da ake zargi da aikata laifukan yaki a Gaza.

A cewar wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Anadolu ya wallafa, lauyoyin cibiyar kare hakkin jama’a da cibiyar kare hakkin bil’adama ta Falasdinu sun gabatar da rahoto ga sashin yaki da ta’addanci na ‘yan sandan birnin London, wanda kuma ke binciken laifukan yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref

Matainakin shugaban kasar kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya bayyana cewa, daukewa Iran takunkuman zalunci wadanda kasashen yamma suka dora mata na daga cikin asalin hakkin kasar da aka tauye.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Aref yana fadar haka a jiya Asabar, ya kuma kara da cewa, kasar Iran ba zata manta da hakkin kasar wanda Amurka ta take tun farkon nasarar juyin juya halin kasar shekaru 46 zuwa yanzu ba, amma duk da haka sun bata damar tattaunawa.  Yace: Muna son mu nunawa duniya kan cewa har yanzun muna hakuri, amma ba zamu taba manta da zaluncin da aka yi mana ba.   Mataimakin shugaban yana maganar ficewar kasar Amurka daga yarjeniyar JCPOA da kuma dorawa kasar takunkuman tattalin arziki mafi muni da nufin kifar da gwamnatin kasar. Yace dukkan takunkuman tattalin arzikin da gwamnatocin kasar Amurka ta dorawa kasar tun bayan nasarar juyin juya halin kasar shekaru 46 da suka gabata basa bisa ka’ida.  Mataimakin shugaban kasar yana fadar haka ne bayan da ministan harkokin wajen kasar Abbas Aragchi ya kammala zagaye na farko na tattaunawa ba kai tsaye ba kan shirin makamacin Nukliya na kasar da tokwaransa na kasar Amurka Steve Witkoff a kasar Omman tare da ministan harkokin wajen kasar Omman Badr Hamad Al-Busaidi a matsayin mai shiga tsakani.

Iran Ta Godewa Omman Da Shiryawa Da Kuma Gudanar Da Tattaunawa  Tsakanin Amurka Da Iran

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza
  • An Kashe Sojojin Yahudawa A Gaza A Yayinda Wasu Da Dam Suka Ji Rauni
  • Rundunar “Gulani” Ta Shiga Sahun Masu Kin Amincewa Da Yaki
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • ‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Hada Makamai A Kano
  • Jiragen Saman Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Luguden Wuta Kan Asibitin Baptist Da Ke Gaza
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen