Reshen soja na kungiyar Hamas wato rundunar Izzuddin Qassam, ya gargadi iyalan fursinonin yahudawan Sahyoniyya wadanda take tsare da su a Gaza kan cewa yayansu zasu koma hannunsu gawaki, saboda irin yadda HKI take kara yawaita Jefa boma-boman a kan Falasdinawa a Gaza.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto  wani mai magana da yawan dakarun yana fadar haka a wani fai-fai bidiyo da rundunar ta watsa a yanar gizo a jiya talata.

Dakarun suna kira ga iyalan yahudawan da su yi shirin karban gawakin yayansu a cikin akwatunan gawaki, wannan kuma saboda yadda jiragen yakin HKI suke kai hare-hare babu kakkautawa kan gaza ba tare da bambanta tsakanin  yara da mata da sauransu ba.

Sakon Bidiyon yana cewa (Ya ku iyalan fursinonin ku yi shirin karban gawakin yan uwanku cikin akwatunan gawaki, tare da ganin yadda naman jikinsu a tarwatse, saboda gwamnatinku ta yanke shawarar kashe su a Gaza, don haka ku jira ku gani’.

Wannan sanarwan tana zuwa ne bayan da kungiyar ta bada sanarwan cewa ta kasa samun labarin bangaren dakarun kungiyar wadanda suke kula fursinoni don sanin halin da suke ciki, don mai yuwa an halaksu.

Daga cikin fursinonin da dakarun suka rasa inda yake dai, shi ne Edan Alexander bayahude kuma ba’amerike.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta

Wata ’yar kasar Jamus mai suna Alexandra Hildebrandt mai shekara 66 ta ja hankalin jama’a bayan ta haifi ɗanta na 10 ba tare da maganin haihuwa ba.

Haihuwar ta faru ne a ranar 19 ga Maris a Asibitin Charité da ke Berlin da taimakon likita.

Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato

Ta bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da ta yi da Jaridar TODAY.com a ranar Laraba, 26 ga watan Maris.

A cewar Hildebrandt, ta rawa wa jaririn suna Philipp, wanda ya zo da nauyin kilo 7, kuma yana cikin koshin lafiya.

Ta bayyana shi a matsayin wanda ya dace da ’ya’yanta da ke da yawa, wanda ya haɗa da yara masu shekaru tsakanin 2 zuwa 46.

“Babban iyali ba kawai wani abu ne mai ban mamaki ba, amma duk da haka, yana da mahimmanci don renon yara yadda ya kamata,” in ji ta a cikin imel.

Hildebrandt, wanda ke kula da gidan tarihi na Wall Museum a Checkpoint Charlie a Berlin, ba bakon abu ba ne wajen jan hankalin jama’a.

Rayuwarta cike take da tarihi, domin zama uwa a wurinta abin mamaki ne.

Duk da shekarunta, ta nace cewa ciki ba a tsara shi ta hanyar kimiyya, amma ya faru ne ta dabi’a.

Mahaifiyar ta bayyana cewa, tana rayuwa cikin matukar aiki.

Kafin haihuwar Philipp, ta bayyana wa Jaridar Jamus ta Bild cewa, “Ina cin abinci cikin koshin lafiya, ina iya yin ninkaya tsawon awa guda a matsayin motsa jiki kuma ina tafiyar tsawon awa biyu.”

Likitanta, Dokta Wolfgang Henrich ya tabbatar da cewa, cikin nata ya daidaita, yana mai bayyana shi a matsayin cikin da ba shi da matsala sosai,” kodayake Hildebrandt ta yi haihuwa takwas a baya duk ta hanyar tiyata.

‘Ya’ayanta 10 sun hada da tagwaye, Elisabeth da Madimilian, dukansu shekarunsu 12, wadanda suke nuna cewa, rayuwar Hildebrandt a matsayin uwa cike take da matakai iri-iri.

Amma haihuwar ’ya’ya a irin waɗannan shekarun na tsufa ba kowa ba ne ke samun hakan.

Henrich ya yi gargaɗin cewa, masu juna biyu a shekarun tsufa na rayuwa cikin haɗari.

Ya bayyana cewa, “matsaloli irin su hawan jini da haihuwar jariri kafin mako 37 da kuma al’amurran da suka shafi zuciya da jijiyoyin jini yawanci na karuwa da shekaru”.

Ta ce, tana ta samun sakonnin taya murna da soyayya daga abokanta da danginta bayan sanar da haihuwar Philipp.

“Na yi ta samun sakonnin fatan alheri,” in ji ta TODAY.com.

A halin da ake ciki, masana kiwon lafiya sun yi imanin cewa, ba koyaushe shekaru suke taƙaita batun haihuwa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa
  • Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Shirin Sakin Dukkanin Fursunonin Isra’ila Bisa Sharuddan Da Ta Gindaya
  •  Aljeriya Ta Kori Jami’an Diflomasiyya Faransa 12
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • ’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta
  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza