Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda
Published: 16th, April 2025 GMT
Wani matashi, Umar Auwal, mai shekaru 20 da ya yi iƙirarin kashe mutane ya miƙa kansa ga rundunar ’yan sanda a Jihar Kano.
Matashin mai inkiyar ‘Abba Dujal’ ya ce ya miƙa kansa ga mahukunta ne sakamakon rashin samun kwanciyar hankali tun bayan ta’addancin da ya aikata a bayan nan.
Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15 kan laifin rashawa Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — GandujeHakan dai na ƙunshe ne cikin wani saƙon murya da kakakin ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Da yake amsa tambayoyi, Abba Dujal ya yi iƙirarin aikata manyan laifuffuka da suka haɗa da kisan kai, fashi da makami da kuma satar babur da wayoyin hannu.
Matashin ya yi iƙirarin kashe wani mutum mai suna ‘Boka’ a unguwar Sabon Gari ta Kano, inda ya sace wayarsa Infinix Hot 40i, ya kuma sayar da ita a kan N40,000.
Haka zalika, ya bayyana yadda ya kashe wani mutum a unguwar Kurna da ke Kano, inda ya arce da wayarsa ƙirar Samsung S26 da ya sayar a kan N160,000.
A Jigawa kuwa, ya ce ya kashe wani mutum a karamar hukumar Ringim tare da sace babur ɗinsa da ya sayar da shi a kan N300,000.
Abba Dujal ya ce yanzu haka ya shekara bakwai bai yi sallah ba. Sai dai ya ce an saka shi a Islamiyya amma malamin ya dawo da shi gida saboda fitinar da yake a makarantar.
A fannin karatun boko kuma, Abba Dujal ya ce ya taɓa shiga firamare amma daga nan bai ƙara gaba ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Zargin Ganduje: Za mu sanar da lokacin yanke hukunci —Kotu
Mai Shari’a Amina Adamu Aliyu ta Babbar Kotun ta Jihar Kano ta ce za ta yanke hukunci nan gaba a shari’ar cin hanci da rashawa da ake yi wa Shugaban Jam’iyyar APC na Kasa, Abdullahi Ganduje, da matarsa Hafsat, da wasu mutane da kamfanoni shida.
Gwamnatin Jihar Kano ta tuhumi waɗannan mutane da kamfanoni da laifuka guda takwas da suka haɗa da karɓar rashawa, yin amfani da kuɗin jama’a ta haramtacciyar hanya, da kuma satar kuɗin gwamnati.
Ganduje ya yi gwamnan Jihar Kano daga shekarar 2015 zuwa 2023.
Lauyan Ganduje ya roki kotu da ta ba shi karin lokaci a shari’ar amma lauyan gwamnati ya soke wannan roko kuma ya bukaci kotu da ta yi watsi da shi.
Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ’yan jarida su daina kawo rahoton ayyukan ’yan ta’adda Hisbah ta kama matashi yana ‘lalata’ da Akuya a KanoLauyoyin wasu mutane da kamfanoni da ake tuhuma a shari’ar sun kuma gabatar da wasu batutuwa kuma sun roki kotu da ta na su gaskiya tare da umartar gwamnati da ta biya su diyya.
Mai Shari’a Amina Adamu Aliyu ta dakatar da sauraron ƙarar kuma ta ce za ta sanar da dukkan waɗanda abin ya shafa ranar da za ta yanke hukuncinta daga baya.