Aminiya:
2025-04-19@00:30:42 GMT

An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato

Published: 16th, April 2025 GMT

Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, ya sanar da haramta kiwo da daddare tare da taƙaita amfani da babura a faɗin jihar sakamakon yawaitar hare-haren da ake kai wa a wasu sassan jihar.

A cikin wani jawabi da ya yi a jihar a ranar Laraba, Mutfwang ya bayyana hare-haren a matsayin “ayyukan ta’addanci” da ke da nufin tarwatsa mazauna yankin da kuma tauye hakkinsu na kasancewa cikin lumana a yankunansu.

Gwamnan ya kuma haramta safarar shanu cikin ababen hawa bayan karfe 7 na dare.

Ya kuma hana amfani da babura daga karfe 7 na yamma zuwa karfe 6 na safe a faɗin jihar har na wani tsawon lokaci inda ya ce umarnin zai fara aiki ne nan take.

Ya ce ” Ina jinjinawa masu ba da agajin gaggawa da jami’an tsaro bisa gaggarumin matakin da suka ɗauka, ina kuma gode wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya umurci jami’an tsaro da su tabbatar da adalci cikin gaggawa.”

Muftwang ya ce dole ne al’ummomi su ba da himma wajen kare kansu a cikin iyakokin da doka ta tanada.

Ya ce ”Ina kira ga sarakunan gargajiya da shugabannin matasa da su sake farfaɗo da sintiri tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro. Dole ne mu haɗa kai don kare ƙasarmu, domin tabbatar adalci yayin da mu ke la’akari da kiyaye dokokin ƙasa.”

Aƙalla mutane 50 ne rahotanni suka ce an kashe bayan wasu ƴan bindiga sun kai hari ƙauyen Kimakpa da ke gundumar Miango a ƙaramar hukumar Bassa ta jihar a ranar 14 ga watan Afrilu.

Harin ya zo ne makonni biyu kacal bayan da wasu ƴan bindiga suka kashe mazauna ƙauyuka biyar a ƙananan hukumomin Bokkos da Mangu.

Hukumomin ƙasar dai na ci gaba da ƙoƙarin ganin sun daƙile hare-hare a jihar da aka daɗe ana fama da rikicin kabilanci da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Kira Ga Jihohi Da Su Kara Samar Da Ingantacciyar Hanyar Kiyon Lafiya

An bukaci gwamnatocin jihohi da su kara samar da tsarin kula da kiwon lafiya na bai daya (UHC) ga ‘yan kasa domin tabbatar da samar da ingantaccen kiwon lafiya a kasar.

 

Jami’ar Ayyuka, Kula da Lafiya ta Duniya ga Mata a Lafiya ta Duniya, Najeriya (WGH), Dokta Sienne Oluwatosin Orogun, ta yi wannan kiran a wani taro mai taken “Amfani da Dabaru da Tsarin Gida don Haɓaka Tsarin Kiwon Lafiyar Duniya” a Ilorin, jihar Kwara.

 

A cewarta akwai tsare-tsare da aka tsara don samar da inshorar lafiya mai araha ga masu rauni a cikin al’umma, ta kara da cewa aiwatar da ingantaccen aiki ya kasance kalubale.

 

Tun da farko a nata jawabin, kwamishiniyar lafiya ta jihar Kwara, Dokta Amina El-Imam, ta jaddada cewa hukumar kula da lafiya ta duniya (UHC) ita ce manufar tabbatar da cewa dukkan mutane sun samu cikakkiyar kulawar kiwon lafiya da suke bukata ba tare da fuskantar matsalar kudi ba.

 

Dokta El-Imam ya nuna damuwarsa kan kalubale kamar matsalolin kudade da karancin ma’aikata.

 

Ta ci gaba da cewa gwamnatin jihar na kokarin ganin an cimma kashi 15 cikin 100 na kasafin kudin jihar a fannin kiwon lafiya, da inganta iya aiki da kuma rike hannun mafi kyawu a cikin bukatun duniya.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilan Da Suke Sa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Ci Gaba Da Tafka Asara A Halin Yanzu
  • Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia
  • Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun
  • Bai Wa Shanu Guba: Sojoji Sun Shiga Tsakani Domin Dakile Yunkurin Ramuwar Gayya A Filato
  • An Yi Kira Ga Jihohi Da Su Kara Samar Da Ingantacciyar Hanyar Kiyon Lafiya
  • An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Garambawul A Fannin Kiwon Lafiya