Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano
Published: 17th, April 2025 GMT
Hukumar Hisbah a Jihar Kano ta cika hannu da wani matashi da aka gani a wani yanayi mai kamanceceniya da baɗala da wata Akuya, lamarin da ya janyo cece-kuce a dandalin sada zumunta.
Matashin, Shamsu Yakubu mai shekaru 24 da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa ta Kano, ya shiga hannu ne bayan ɓullar wani bidiyonsa a dandalan sada zumunta musamman TikTok yana tsotsar farjin wata Akuya.
A cikin bidiyon da wani yake ɗaukarsa wanda ya yaɗu sosai a soshiyal midiya, an hasko matashin a wannan yanayin mai kama da baɗala tare da Akuyar.
Sai dai yayin da yake amsa tambayoyin mahukunta, matashin ya yi iƙirarin aikata hakan da nufin neman suna domin samun ɗaukaka ta dandalin sada zumunta.
Wannan lamari da ya fusata mazauna yankin ya sanya suka yi yunƙurin ɗaukar mataki a hannunsu, amma aka yi sa’a wani jami’in Hisbah ya tari hanzarinsu kuma aka cafke shi.
A yayin shan titsiye, matashin ya musanta zargin da ake yi masa, yana rantsuwa da Allah cewa bai tsotsi Akuyar ba.
“Na rantse da Allah ban tsotsi Akuyar ba, bakina kawai na kai kusa da wurin,” a cewarsa.
Matashin ya kuma bayyana cewa wannan shi ne karon farko da ya aikata irin wannan lamari yana mai nadamar cewa ba zai ƙara ba.
Sai dai duk da ya musanta cewa ba ya ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ko kayan maye, Hukumar Hisbah ta umarci a yi masa gwajin ƙwaƙwalwa.
Da yake martani kan lamarin, Mataimakin Kwamandan Hisbah, Sheikh Aminuddeen Abubakar, ya yi Allah wadai yana mai cewa wannan abun kunya ya saɓa wa tarbiyya da koyarwar addinin Islama
“Abun takaici ne mutum ɗan Musulmi ya faɗa wannan abun kunya domin neman suna,” in ji Sheikh Aminuddeen.
Haka kuma, ya ce za a kai Akuyar Asibitin Dabbobi domin duba lafiyarta.
Sheikh Aminuddeen ya gargaɗi masu ƙoƙarin neman suna da wallafe-wallafen hofi marasa kan gado.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Akuya Baɗala Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Tana Daukan Tattaunawarta Da Amurka Da Muhimmanci Don Neman Warware Takaddamar Shirinta Na Makamashin Nukiliya
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bada muhimmanci game da tattaunawa da ita kuma a shirye take ta magance matsaloli da takaddamar da ake yi kan Shirin makamashin nukiliyarta
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran Muhammad Kazim Gharibabadi ya bayyana cewa: zagayen farko na tattaunawar da ba na kai tsaye ba da aka gudanar a birnin Muscat na kasar Oman tsakanin Iran da Amurka, ba a samu wani babban sabani ba, kuma an yi shi ne domin tantance muhimmancin bangarorin biyu da kuma bayyana matsayinsu.
Gharibabadi ya kara da cewa: A wannan zagayen tattaunawan Iran ta nuna muhimmancin tattaunawar da kuma rashin son bata lokaci, yana mai cewa amincewa da shawarar da Amurka ta yi na gudanar da shawarwari ba wai saboda raunin Iran ba ne, sai dai abin da ya bayyana a matsayin karfinta da gazawar takunkuminta.
Gharibabadi ya tabbatar da cewa a ko da yaushe kasarsa a shirye take ta kawar da damuwar da ake da ita game da shirinta na makamashin nukiliya, yana mai jaddada cewa mallakar makamin nukiliya ba shi da wani matsayi a koyarwar tsaron Iran. Ya kuma yi nuni da cewa shirin inganta sinadarin uranium gaba dayansa na cikin gida ne, babu wata sabawa ka’ida, kuma ba zata tattaunawa kan tace sinadarin na uranium ba.