Aminiya:
2025-04-19@05:34:30 GMT

Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta

Published: 17th, April 2025 GMT

Gwmanatin Sojin Nijar ta sanar da cewa sun sasanta da Gwmanatin Najeriya.

Hakan ta faru ne bayan ziyarar aiki da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya kai birnin Yamai, fadar gwamnatin Nijar.

Bayan sanya hannu kan takardar, Ministan Harkokin Wajen Nijar, Bakary You Sangare, ya bayyana cewa, “da ma Najeriya ’yan uwanmu ne, duk wanda ya ce zai raba  Nijar da Najeriya, shi da kansa ya san ba gaskiya ba ne, abu ne na Allah.

Allah Ne Ya haɗa wannan zumunta ka, babu wanda ya isa ya raba ta.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin sojin Nijar Najeriya Nijar Tuggar Yamai

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye ta hanyar hadin gwiwa da inganta fasaha.

 

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris ne ya bayar da wannan tabbacin a taron manema labarai na 2025 da aka gudanar a cibiyar ‘yan jarida ta kasa da ke Abuja ranar Alhamis.

 

Da yake jawabi bayan dawowar sa daga taron kungiyar masu yada labarai na duniya (NAB) a birnin Las Vegas na kasar Amurka, ministan ya ce taron mai taken “Fasahar, The Trend, The Future,” ya samar da wani dandali na yin cudanya da masu ruwa da tsaki a duniya kan sabbin abubuwa da suka tsara makomar watsa shirye-shirye.

 

Ya ce shigarsa wani bangare ne na kokarin da gwamnatin Tinubu ke yi na bunkasa fasahar na bangaren yada labarai na Najeriya.

 

A cewarsa, “wannan zai tabbatar da kudurin gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na ganin an samu sauyi mai dorewa a fagen yada labaran Najeriya.”

 

Ministan ya kuma bayyana irin rawar da ya taka a taron ‘yan kasuwan Najeriya da aka gudanar a birnin Paris na kasar Faransa, inda ya gana da jami’an UNESCO kan shirin kafa cibiyar koyar da kafafen yada labarai da wayar da kan jama’a a Abuja. Ana sa ran Cibiyar da aka tsara za ta inganta tare da samarda ƙwararrun ‘yan jarida da haɓaka ayyukan watsa labarai masu dacewa.

 

Ya kuma kara jaddada cewa shirin gabatar da jawabai na ministocin da ake yi da kuma tarukan da aka shirya yi a fadin kasar nan na da nufin tabbatar da gaskiya, hada kan jama’a, da kara dankon zumunci tsakanin gwamnati da ‘yan kasa.

 

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Ministan Wutar Lantarki, Cif Adebayo Adelabu, wanda ya bayyana muhimman ci gaban da aka samu a fannin samar da wutar lantarki, wanda ya yi daidai da ajandar gwamnati na bunkasa masana’antu a Najeriya da inganta samar da wutar lantarki a fadin kasar.

 

Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Za A Gudanar Da Zagaye Na Biyu Na Tattaunawar Iran Da Amurka A Birnin Roma Ne
  • Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta
  • Ba a taɓa Dimokraɗiyya mai tsafta a Najeriya kamar mulkin Tinubu ba – Matawalle
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
  • Wata Cibiyar Kare Hakkin Bil’Adama Ta Bukaci Kama Jami’in Haramtacciyar Kasar Isra’ila A Kasar Birtaniya
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta
  • Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ’yan jarida su daina kawo rahoton ayyukan ’yan ta’adda
  • Ministan harkokin wajen Najeriya Ya kai ziyara Nijar
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu ranar Juma’a da Litinin