WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka
Published: 17th, April 2025 GMT
Kungiyar kasuwanci ta duniya ta bayyana cewa, za a sami raguwar hajar da za a yi kasuwancinta a duniya da kaso 0.2% saboda Karin kudin fito da Amurka ta yi.
Rahoton kungiyar kasuwancin ta duniya wanda aka fitar da shi a ranar Litinin din da ta gabata ta gina shi ne akan yadda tafiyar kasuwanci za ta kasance daga 2025-2026, wanda aka tsammaci zai rika samun bunkasa, sai dai kuma Karin kudaden fito da Donald Trump ya yi, ya sa kungiyar ta sauya hasashen da ta yi a baya.
Cinikayya ta kayayyaki zai ta yi baya da kaso 1.5% idan har Donald Trump din ya yi aiki da sabuwar siyasar tasa ta haraji.
Shugaban na Amurka ya dakatar da aiki da sabon salon haraji na tsawon kwanaki 90, domin bai wa kasashe 70 na duniya damar sauya yadda suke cinikayya da Amurka. Karin da Trump din ya yi wa kayan China ya kai kaso 145%, yayin da ya dan saukaka shi akan kasashen Canada da Mexico.
Babbar daraktar kungiyar kasuwancin ta duniya Ngozi Okonjo -Iweala ta sanar da cewa; Duk da cewa an sami tsaikon aiwatar da sabon haraji, amma duk da haka da akwai rashin tabbaci a kasuwannnin na duniya da hakan a kanshi yake a matsayin wani cikas na ci gaba.
Wannan dai ba shi ne karon farko da kungiyar ta kasuwanci ta duniya tare da Asusun Bayar Da Lamuni su ka yi gargadi akan yadda za a sami koma baya a fagen kasuwanci da cinikayya a duniya ba, saboda matakin na kasar Amurka na Karin harajin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Damu Akan Mummunan Yanayin Da Mutanen Al-Fasha Na Sudan Suke Ciki
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Dr. Isma’ila Baka’i ya bayyana cewa; Yanayin da mutanen garin al-fasha na Sudan suke ciki ya yi muni, tare da yin kira da a kawo karshe killace garin da aka yi da kuma bai wa fararen hula kariya.
Mayakan “Rundunar Kai Daukin Gaggawa” dake fada da sojojin Sudan ta shimfida ikonta akan sansanin ‘yan hijira na “Zamzam’ bayan kwanaki na barkewar fada a kusa da birnin al-fasha.
Daruruwan mutane ne su ka rasa rayukansu yayin da wani adadi mai yawa na ‘yan hijirar ya jikkata.
Dr. Isma’ila Baka’i ya bayyana matsayar jamhuriyar musulunci ta Iran na nuna cikakken goyon bayan Sudan a matsayin dunkulalliyar kasa.
A bisa kididdigar MDD a kalla mutane 300 aka kashe a kusa da wannan sansanin na Zamzam a fadan da aka yi a ranakun Juma’a da Asabar.
Har ila yau MDD ta kuma ce,wani adadin na mazauna yankunan Zamzan da Abu Shok da garin al-Fashar da sun kai 400,000 an tilasta musu ficewa daga gidajensu. Haka nan kuma wasu mutanen da sun kai miliyan 13 sun gudu, zuwa inda za su sami aminci a cikin gida da kuma wajen kasar.