MDD Ta Nuna Damuwarta Akan Kokarin Sake Raba Kasar Sudan Gida Biyu
Published: 17th, April 2025 GMT
Mai Magana da yawun kakakin babban magatakardar MDD Steven Dujarric ya nuna damuwa akan sanar da kafa wata gwamnati ta daban da shugaban rundunar daukin gaggawa Hamidati Duklu ya yi a shekaran jiya Laraba.
Shugaban rundunar kai daukin gaggawar ta Sudan wanda yake fada da sojojin kasar ya shelanta kafa sabuwar gwamnati wacce ya ce za ta kasance ta zaman lafiya da hadin kai ce.
Hamidati wanda ya gabatar da jawabi a lokacin da ake tunawa da zagayowar cikar shekaru 3 da fara yaki a kasar ta Sudan, ya kuma ce; A halin yanzu suna Shirin buga kudaden Sudan na daban, da kuma samar da wasu muhimman takardu na aikin gwamnati.
Wannan sanarwar daga shugaban rundunar kai daukin gaggawar ta Sudan yana zuwa ne bayan da sojojin Sudan su ka kori mafi yawancin mayakansa daga birnin Khartum da kuma wasu muhimman wuraren a kasar ta Sudan.
A watan da ya shude ne dai shugaban dakarun kai daukin gaggawa na Sudan din ya halarci wani taro a kasar Kenya da ya shelanta kafa gwamnatin bayan fage tare da wasu kungiyoyi da suke goya masa baya.
Shi dai Hamidati yana fuskantar zarge-zarge daga kungiyoyin kare hakkin bil’adama na kasa da kasa akan aikata laifuka da su ka hada da yi wa mata fyade da cin zarafin kananan yara.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya
Gwamnatin kasar Amurka ta bada sanarwan cewa zata rufe wasu daga cikin ofisoshin jakadancinta har kimani 30 a kasashen duniya, amma mafi yawansu a kasashen Afirka.
Shafin yanar gizo na labarai Afrika News ya nakalto ma’aikatar harkokin wajen kasar Amurkan na fadar cewa gwamnatin shugaban Trump tana son ta rage yawan kashe kudade a ma’aikatar don amfani da su a cikin gida.
Labarin ya kara da cewa gwamnatin tana son rage kudaden da ma’aikatar take kashewa a kan ofisoshin jakadunsu da kasha 50% da kuma rage tallafin da take bawa wasu kungiyoyi a wadan nan kasashe har da kasha 75%.
Labarin ya kara da cewa kasashen da shirin ya shafa dai akwai Lesotho, Eritrea, Afrika ta tsakiya, Congo Brazavile, Gambia, Sudan ta kudu,. Banda wadannan za’a rufe kananan ofisoshin jakadanci da ke birnin Durban na Afrika ta kudu, da kuma na Douala, da ke kasar Cameroon. Labarin yace ayyukan wadannan ofisoshin jakadanci zasu kuma ga kasashe makobta.
A kasahen turai da Asiya kuma Amurka zata rufe ofisoshin jakadancinta a tsibirin Malta, Luxembourg, da kuma wasu kananan ofisoshin jakadancin kasar a tarayyar Turai da Asiya.