Aminiya:
2025-04-19@05:32:40 GMT

NAJERIYA A YAU: Ainihin Abin Da Ke Hana Matan Arewa Koyon Ilimin Kimiyya

Published: 17th, April 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Dakta Zainab Muhammad ’yar Arewacin Najeriya ce da ta jajirce tare da ƙudirin cika burinta na karantar fannin kimiyya duk da ƙalubalen da matan yankin suke fuskanta wurin karantar fannin.

Dakta Zainab ba kimiyya kawai ta karanta ba, ta karanci ɗaya daga cikin kimiyyoyin da ake ganin sun fi kowanne wahala, wanda a mafi yawan lokuta, ba mata kaɗai ba, har da mazan ma na ƙaurace wa karatar sa.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo

Zainab ƙwararriyar likita ce wacce ta shahara wajen kula da marasa lafiya a asibitoci.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kimiyya matan Arewa

এছাড়াও পড়ুন:

BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano

Cibiyar Nazarin Dimokuradiyya ta Aminu Kano a Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta shirya taron shekara-shekara karo na 23 don tunawa da cika shekaru 42 da rasuwar Malam Aminu Kano.

 

 

A nasa jawabin, Shugaban jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya jaddada muhimmancin taron shekara-shekara wajen kiyaye manufofin da Malam Aminu Kano ya tsaya a kai.

 

Farfesa Haruna Musa wanda mataimakin shugaban jami’ar kula da harkokin ilimi ya wakilta, ya bayyana cewa jerin laccoci an yi niyya ne don ba da damar fahimtar juna dangane da yanayin tarihi.

 

“A ci gaba da kokarin da jami’ar mu ke yi na karfafa al’adun dimokuradiyyar Najeriya, muna gayyatar manyan mutane duk shekara don gabatar da laccoci a gidan Mambayya kan batutuwan da suka shafi kasa baki daya.

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabiru Yusuf, ya bayyana Malam Aminu Kano a matsayin wani hamshakin mai neman sauyi na Afirka, kuma dan gwagwarmayar siyasa mai jajircewa, wanda rayuwarsa ke ci gaba da zaburar da al’umma.

 

 

Wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya jaddada cewa taken taron ya dace saboda halin da kasar nan ke ciki.

 

A nasa jawabin, Farfesa Kabiru Isa Dandago ya gabatar da kasida mai taken “Siyasar Gyaran Haraji a Najeriya: Tsammani da Gaskiya.

 

Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa taron tunawa da marigayin ya hada masana, masana siyasa, da shugabannin kungiyoyin farar hula, inda suka yi bita a kan rayuwar marigayi dan kishin kasa, malami, dan juyin juya hali.

 

KHADIJAH ALIYU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta
  • BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano
  • Ba a taɓa Dimokraɗiyya mai tsafta a Najeriya kamar mulkin Tinubu ba – Matawalle
  • Fani-Kayode ya zargi Isra’ila da Hannu a tashe-tashen hankula a Najeriya
  • ’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta
  • Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu
  • Ministan harkokin wajen Najeriya Ya kai ziyara Nijar