Hukumar EFCC Ta Kama Mutane 40 da Ake Zargi da Damfarar Intanet
Published: 17th, April 2025 GMT
Jami’an hukumar shiyyar Kaduna na hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, sun kama wasu mutane arba’in da ake zargi da damfarar yanar gizo a kananan hukumomin Bida da Minna na jihar Neja.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban hukumar EFCC, Dele Oyewale ya raba wa manema labarai a Minna babban birnin jihar Neja.
A cewarsa an kama su ne biyo bayan sahihan bayanan sirri da ke alakanta su da ayyukan damfara na intanet.
Kayayyakin da aka kwato daga hannunsu sun hada da motoci uku, na’urorin samar da wutar lantarki guda takwas, na’urar sanyaya daki samfurin Hisense guda daya, na’urorin sarrafa wutar lantarki guda biyu, babura 10, kwamfutocin tafi da gidanka guda takwas, na’urar magana ta bluetooth hudu da wayoyin android 60 da dai sauran kayyaki.
Za a gurfanar da wadanda ake zargin zuwa kotu da zarar an kammala bincike.
PR ALIYU LAWAL.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Wata Cibiyar Kare Hakkin Bil’Adama Ta Bukaci Kama Jami’in Haramtacciyar Kasar Isra’ila A Kasar Birtaniya
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Hind Rajab ta yi kira ga Birtaniya da ta kama ministan harkokin wajen haramtacciyar kasar Isra’ila
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Hind Rajab ta gabatar da bukatar fitar da sammacin kame ministan harkokin wajen haramtacciyar kasar Isra’ila Gideon Sa’ar da yake ziyara a Birtaniya.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo cewa: Cibiyar Hind Rajab Foundation da ta mayar da hankali kan neman gurfanar da sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila da ake zargi da aikata laifukan yaki, ta mika bukatar kama Gideon Sa’ar a birnin Landan na Birtaniya.
Kafofin watsa labaran haramtacciyar kasar Isra’ila sun jiyo ofishin ministan harkokin wajen haramtacciyar kasar Isra’ila na cewa babu wata niyyar takaita ziyarar Sa’ar a Biritaniya ko kuma sauya jadawalinsa sakamakon wannan bukata.
A cikin wata sanarwa da cibiyar Hind Rajab ta fitar ta ce: Tana ci gaba da kokarin ganin an fitar da sammacin gaggawa kan kame Sa’ar, mamba a majalisar ministocin tsaron gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila.
Cibiyar ta yi ikirarin cewa: Gideon Sa’ar ya taimaka tare da karfafa aiwatar da laifuka da suka hada da keta dokokin jin kai na kasa da kasa a Falasdinu, ciki har da azabtarwa, kisa da gangan da kuma lalata dukiyoyi.