Aminiya:
2025-04-19@07:10:22 GMT

’Yan bindiga sun sace makiyaya 5, da shanu 1,200 a Kaduna

Published: 17th, April 2025 GMT

Mazauna gundumar Kufana a Ƙaramar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna sun shiga cikin fargaba sakamakon jerin hare-haren ’yan bindiga da ya yi sanadiyyar sace mutane biyar da kuma kwashe shanu 1,200 cikin kwanaki hudu.

Babban Jami’in Gundumar, Mista Stephen Maikori, ya tabbatar da faruwar hare-haren a ranar Laraba.

A cewarsa, lamari na farko ya faru ne a daren Talata, 8 ga Afrilu, 2025, lokacin da ’yan bindiga suka kai hari kauyen Mashigi Boka-Libere, wani matsugunin Fulani, da misalin karfe 10 na dare.

Maikori ya ce maharan sun kwashe garken shanu guda 12, inda kowanne garke yake da kimanin shanu 100, wanda ya kai jimillar dabbobi 1,200.

Dangote: Har yanzu gidajen mai ba su rage farashin mai ba Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta

Ya ce maharan sun wuce ta kauyen Dogon Noma, inda suka kai hari ga mazauna suka kuma sace babura biyu daga hannun Mista Abednego Samuel da Mista Danjuma John.

A ranar Litinin, 7 ga Afrilu, da misalin karfe 6 na safe, an sace mutane uku daga Ungwan Kaje Afogo.

Maikori ya ce wani harin kuma ya faru a daren Alhamis, 10 ga Afrilu, a al’ummar Afogo Gari, inda aka sace Miss Patience Audi da Mista Arewa Anthony.

Ya ce, “Muna ci gaba da tuntubar jami’an tsaro da iyalai da abin ya shafa.”

Kokarin da aka yi na tuntubar kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, bai yi nasara ba saboda yana cikin taro kuma bai amsa kiran waya ba a lokacin da ake tattara wannan rahoto.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Gidan Iyayen Sanata Natasha A Kogi

“Na gode Allah, babu wanda ya jikkata, kuma an kai rahoton lamarin ofishin ‘yansanda.”

Ofishin yaɗa labaranta ya buƙaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, inda ya ce “ƙoƙarinta na kare gaskiya da wakiltar al’ummarta bai kamata a mayar da shi barazana ko tashin hankali ba.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Gidan Iyayen Sanata Natasha A Kogi
  • Bai Wa Shanu Guba: Sojoji Sun Shiga Tsakani Domin Dakile Yunkurin Ramuwar Gayya A Filato
  • Yara Kimani 3,500 Ne Suka Rasa Rayukansu A Taken Medeteranin A Shekaru 10 Da Suka Gabata
  • An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato
  • Hamas ta bukaci hadin kan duniya domin kawo karshen kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza
  • KADGIS Za Ta Yi Amfani Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna
  • KADGIS Ta Samar Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Manoma 7 A Wani Sabon Hari A Benuwe