Aminiya:
2025-04-19@07:06:25 GMT

Gwamnatin Yobe ta sayo hatsi don tunkarar kakar bana

Published: 18th, April 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Yobe ƙarƙashin jagorancin Gwamna Mai Mala Buni  ta sayo ton 2,000 na hatsi iri-iri domin ƙarfafa samar da abinci da kuma tabbatar da shirin tunkarar kakar bana a matsayin gudun ko ta kwana.

A cikin wata sanarwa da Yusuf Ali, mai bada shawara ta musamman kan harkokin dabarun sadarwa na zamani (SSA) ga gwamna Buni ya ce,  Kwamishinan ma’aikatar noma da albarkatun ƙasa, Ali Mustapha Goniri, ya kai ziyarar duba irin hatsin a shagunan bunƙasa noma na jiha  da ke kan titin Gujba da ke Damaturu.

’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista ISWAP sun ruguza gadar Mandafuma a Borno

Da yake zantawa da manema labarai a yayin ziyarar, Ali Mustapha ya bayyana kyakkyawan fata game da shirin, inda ya jaddada cewa za a raba hatsin ga jama’ar Yobe a cikin gaggawa ko kuma lokacin bazara domin rage matsalar ƙarancin abinci.

Baya ga hatsin, Kwamishinan ya bayyana cewa gwamnati ta sayo nau’o’in sinadarai iri-iri domin tallafa wa manoman rani da kayan lambu.

Ya kuma bayyana shirin raba irin rogo ga manoma a fadin jihar, da nufin farfaɗo da noman na rogo lura da amfanin da ake yi da ita ta fuskoki iri-iri na abinci har ma da sarrafa ta da ake yi ya zuwa garin fulawa don yin abubuwa da ita.

Kwamishinan ya yabawa gwamnatin Gwamna Mai Mala Buni, bisa jajircewa da goyon baya da take bayarwa wajen bunƙasa harkar noma a Jihar Yobe.

Tawagar binciken ta haɗa da babban sakataren ma’aikatar, Barista Muhammed Inuwa Gulani da daraktoci da sauran jami’an ma’aikatar.

Wannan shiri ya ƙara jaddada ƙudirin gwamnatin Jihar Yobe na inganta samar da abinci da kuma baiwa manoma damar bunƙasa harkokin su na noma da nufin samar da ishasshen abinci a faɗin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Mai Mala Buni

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Gombe, Bello Yahaya ya bayar da umarnin tura isassun jami’ai a fadin jihar domin samar da isasshen tsaro kafin bukin Easter, da kuma bayan bikin Easter.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar a Gombe.

 

A cewarsa, an tura jami’an dabarun dakile hare-hare zuwa muhimman wuraren da suka hada da wuraren ibada, wuraren shakatawa, kasuwanni, da sauran wuraren taruwar jama’a.

 

Ya kuma ce, kungiyoyin sintiri da jami’an tsaron cikin za su kasance a kasa domin sanya ido kan ayyukan da kuma gaggauta daukar matakin magance duk wata matsala idan ta taso.

 

Kwamishinan ya lura cewa rundunar tana aiki tare da hadin gwiwar ‘yan uwa jami’an tsaro da masu ruwa da tsaki a cikin al’umma domin kula da su a cikin doka da oda yayin da ake ƙarfafa ‘yan ƙasa su kasance masu bin doka da oda kuma su kai rahoton duk wani abin da ake tuhuma ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

 

HUDU/GOMBE

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ainihin Jarin Wajen Da Sin Ta Yi Amfani Da Shi Ya Karu Da Kaso 13.2% A Maris Na Bana
  • Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Maniyatan Bana A Jigawa
  • AGILE: Gwamnatin Kaduna da Bankin Duniya Na Sauya Rayuwar ’Ya’ya Mata Ta Hanyar Ilimi
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Garambawul A Fannin Kiwon Lafiya