Ba a taɓa Dimokraɗiyya mai tsafta a Najeriya kamar mulkin Tinubu ba – Matawalle
Published: 18th, April 2025 GMT
Karamin Ministan Tsaro a Najeriya Bello Matawalle, ya caccaki masu sukar lamirin Shugaban Kasa Bola Tinubu game da nuna wariya ga yankin Arewacin Najeriya.
Matawalle ya ce Tinubu kadara ne ga Arewa kuma ba shi da fatan da ya wuce ganin ya magance matsalolin da suka addabi yankin kafin 2027.
Cikin wani jawabi da mai taimaka masa kan sha’anin siyasa Ibrahim Danmaliki Gidan Goga ya fita, Matawalle ya ce ba a taba samun lokacin da ake yin dimokradiyya mai tsafta kamar a zamanin Bola Tinubu ba.
’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista
Ya ce duk masu kushe salon mulkinsa kawai suna huce haushin rashi ne da yada farfaganda da karairayi.
“Mutanen Arewa suna da wayewar da sun fi karfin a yaudare su domin cimma wata manufar siyasa. Akwai bukatar mu hada kai waje daya kada mu yarda a yaudare mu.” Inji Matawalle.
Ministan ya ce kamata ya yi a gode ma Tinubu saboda yadda yake inganta yankin Arewa da tsaro kuma ana ganin ci gaba musamman yankin da ya fito na Sokoto-Kebbi-Zamfara.
Bugu da kari ya yaba ma ayyukan ci gaban da yake kawo wa yankin musamman yadda ake shimfida tituna da kokarin kawo ci gaba ga yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bello Matawalle matawalle Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka
Kungiyar Sarakunan Afirka ta jaddada muhimmancin gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen tabbatar da hadin kai da zaman lafiya a Najeriya.
Da yake jawabi a wajen bikin nadin Alhaji Aliyu Dauda a matsayin Sardaunan Najeriya na farko, wanda aka gudanar a Yankari, Jihar Bauchi, Shugaban Kungiyar, Alhaji Ibrahim Haruna, ya bayyana gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen ci gaban kasa.
Alhaji Ibrahim Haruna ya ce, masarautun ba wai kawai suna zama uba ga al’umma ba ne, kawai har ila yau suna bada gagarumar gudunmawa wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.
Ya bayyana cewa goyon baya da gudunmawar da Alhaji Aliyu Dauda ke bayarwa ga masarautun gargajiya, musamman a Arewacin Najeriya, ne ya sa aka zabesa domin karbar wannan gagarumar karramawa.
A jawabinsa na karɓar nadin, Alhaji Aliyu Dauda ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta amince da gudunmuwar da Sarakuna ke badawa ta sanya su a cikin Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.
Ya ce hakan zai ba da damar gudanar da aikinsu cikin ‘yanci ba tare da katsalandan ba.
Bikin ya samu halartar manyan baki, shugabannin al’umma da masoya daga sassa daban-daban na kasar, lamarin da ya zame wata babbar alama ta muhimmancin shugabancin gargajiya a Najeriya.
Rel: Adamu Yusuf